Aminiya:
2025-09-24@11:18:54 GMT

ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki

Published: 10th, August 2025 GMT

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), ta yi gargaɗi cewa za ta iya sake tsunduma yajin aiki saboda gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗauka.

Shugaban ƙungiyar, Christopher Piwuna, ya ce gwamnati ba ta kula da walwalar malamai, ba ta samar da kuɗaɗen gudanar da jami’o’i yadda ya kamata, kuma ba ta aiwatar da yarjejeniyar da suka cimma ba.

Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno Jarumar Kannywood Rahama Sadau ta yi aure

Wannan na zuwa ne bayan Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana cewa “Babu wata jami’a ko malaman ASUU da za su sake shiga yajin aiki” idan aka ci gaba da tattaunawa da kuma cika buƙatun malaman.

Sai dai ASUU ta ce hanyar da za a guji yajin aiki ita ce kawai a cika musu alƙawuran da aka riga aka amince da su.

Ƙungiyar ta bayyana cewa yawancin malamai suna koyarwa da gudanar da bincike ba tare da kayan aiki ko tallafi ba.

Wasu ma ba sa iya biyan kuɗin mota zuwa wajen aiki, biyan buƙatun yau da kullum, har ma da kuɗin makarantar ’ya’yansu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Yajin aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta ɗage ranar dawowarta zuwa 7 ga watan Oktoba

Majalisar Dokoki ta Kasa ta ɗage ranar dawowarta daga hutu zuwa 7 ga watan Oktoba, 2025.

Karin bayani na tafe..

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta hana NUPENG rufe Matatar Ɗangote
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Majalisa ta ɗage ranar dawowarta zuwa 7 ga watan Oktoba
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Kasar Sin Za Ta Shirya Taron Mata Na Duniya A Beijing Yayin Cika Shekaru 30 Da Taron Mata Na 1995
  • Hisbah ta kama masu safarar mata zuwa Saudiyya a Kano
  • Pezeshkian: Kasashen Da Ba Su Cika Alkawura Da Suka Dauka Ba Suke Zargin Iran Kan Rashin Mutanta Yarjejeniyar Nukiliya
  • Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
  • Gwamnan Gombe ya bai wa maharba kyautar motoci da babura don bunƙasa tsaro