ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
Published: 10th, August 2025 GMT
Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), ta yi gargaɗi cewa za ta iya sake tsunduma yajin aiki saboda gwamnati ta kasa cika alƙawuran da ta ɗauka.
Shugaban ƙungiyar, Christopher Piwuna, ya ce gwamnati ba ta kula da walwalar malamai, ba ta samar da kuɗaɗen gudanar da jami’o’i yadda ya kamata, kuma ba ta aiwatar da yarjejeniyar da suka cimma ba.
Wannan na zuwa ne bayan Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ya bayyana cewa “Babu wata jami’a ko malaman ASUU da za su sake shiga yajin aiki” idan aka ci gaba da tattaunawa da kuma cika buƙatun malaman.
Sai dai ASUU ta ce hanyar da za a guji yajin aiki ita ce kawai a cika musu alƙawuran da aka riga aka amince da su.
Ƙungiyar ta bayyana cewa yawancin malamai suna koyarwa da gudanar da bincike ba tare da kayan aiki ko tallafi ba.
Wasu ma ba sa iya biyan kuɗin mota zuwa wajen aiki, biyan buƙatun yau da kullum, har ma da kuɗin makarantar ’ya’yansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Yajin aiki
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027
Jam’iyyar PDP ta ce za ta ɗauki mataki kan wasu mambobinta da ke aikata abubuwan da ke kawo wa jam’iyyar koma baya.
Shugabancin jam’iyyar ya fi damuwa da mambobin da ke bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu don sake tsayawa takara a zaɓen 2027.
Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu Tinubu zai kashe tiriliyan 1.5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin KanoMai magana da yawun jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba, ya ce wasu fitattun mambobin jam’iyyar na yin magana a kafafen watsa labarai tare da ƙalubalantar jam’iyyar.
A cewarsa wasu ma suna bayyana shirinsu na taimaka wa jam’iyyar APC ta samu nasara a zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa.
Ya ce hakan babbar barazana ce ga jam’iyyar PDP.
A cewar kundin tsarin mulkin PDP, babu wani mamba da zai haɗa kai da wata jam’iyya ko ƙungiya don rage ƙarfan jam’iyyar ko gwamnatin PDP.
Ologunagba, ya ƙara da cewa irin waɗannan ayyukan suna haifar da rabuwar kai, rikici da ficewar mambobi daga jam’iyyar, wanda ka iya rage ƙarfinta a zaɓe mai zuwa.
Don haka, Kwamitin Gudanarwa na PDP (NWC) ya yi gargaɗi mai ƙarfi ga waɗanda ke aikata irin waɗannan abubuwa.
Ya kuma buƙaci da su daina, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsauri bisa tsarin jam’iyyar.
Jam’iyyar ta kuma buƙaci dukkanin mambobinta su kasance masu biyayya tare da ci gaba da shiri don tunkarar babban taronta na ƙasa da zai gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, daga 15 zuwa 16 ga Nuwamban 2025.