Aminiya:
2025-08-10@16:46:41 GMT

EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 

Published: 10th, August 2025 GMT

Jami’an Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), sun kai samame a Ɗakin Karatun Olusegun Obasanjo da ke Abeokuta, a Jihar Ogun, inda suka kama wasu matasa da ake zargin ’yan damfara ne.

Samamen ya faru ne da safiyar ranar Lahadi a sashen otal na ɗakin karatun.

’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi

Gidan Obasanjo na musamman yana cikin harabar ɗakin karatun.

Wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, ya nuna yadda wasu matasa ke gudu domin ka da EFCC ta kama su.

Rahotanni sun ce jami’an EFCC sun ƙwace sama da motoci 20 tare da wasu kayayyaki masu daraja.

Wani jami’in EFCC ya shaida wa Aminiya cewa samamen ya samo asali ne daga Ofishin EFCC na Legas.

Daraktan Kamfanin OOPL Ventures, Mista Vitalis Ortese, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana cewa suna ƙoƙarin samun ƙarin bayani daga EFCC.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ce zai yi bincike kafin ya yi wa manema labarai ƙarin bayani.

Wannan na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan jami’an EFCC daga Ofishin Ibadan suka kama mutum 56 da ake zargi da aikata damfara a Intanet a wani otal mai suna K-Hotel da ke Itori, a Jihar Ogun.

An kama ɗaya daga waɗanda ake zargin da bindigogi guda biyu.

EFCC ta kuma ƙwato motoci shida masu tsada, wayoyin salula 89, kwamfutoci, da wasu takardu.

Hukumar ta ce nan ba da jimawa ba za ta gurfanar da dukkanin waɗanda ta kama a gaban kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Damfara Ɗakin Karatu zargi

এছাড়াও পড়ুন:

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Gwamnatin Tarayya ta naɗa Farfesa Mathew Adamu a matsayin sabon mukaddashin Mataimakin Shugaban Jami’ar Abuja, wadda aka sake wa suna zuwa Jami’ar Yakubu Gowon. Farfesa Adamu zai maye gurbin Farfesa Patricia Manko Lar, wadda ta riƙe wannan muƙamin na tsawon watanni shida tun daga Fabrairu 2025. Farfesa Adamu zai fara aiki daga ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025, inda zai riƙe wannan muƙami na tsawon watanni uku.

Farfesa Adamu ƙwararren masani ne a fannin likitancin dabbobi wanda ya fara karatunsa da digiri daga Jami’ar Maiduguri a 1998, sannan ya samu digirin digirgir a Jami’ar Pretoria, Afrika ta Kudu a 2012, an ɗaga darajar shi zuwa cikakken Farfesa a 2019.

Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

A cikin shekaru 27 na aikinsa, Farfesa Adamu ya yi fice a koyarwa, da bincike, da gudanarwa a fannin ilimi. Ya taɓa aiki a matsayin likitan dabbobi na hukumar Youth Corps, sannan ya samu damar koyarwa a Jami’ar Noma ta Makurdi inda ya kai matsayi na Farfesa. Haka kuma ya rike muƙamai da dama ciki har da Mataimakin Tsangaya na Kwalejin Likitocin Dabbobi.

Sanarwar ta bayyana cewa sabon VC zai tallafa wa Kwamitin Gudanarwa don kammala zaɓin cikakken Mataimakin Shugaban Jami’a bisa ga ƙa’idojin doka, kuma an gode wa Farfesa Lar kan jajircewarta a lokacin da ta riƙe mukamin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
  • An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
  • Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Mayar Da Dalibai 184 Da Suka Zo Hutu Daga Cyprus
  • An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo
  • ’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe
  • Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno