Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani
Published: 11th, August 2025 GMT
Wani mutum ya ba da kyautar motarsa da ita kadai gare shi ga wani mai jan baki (alaramma) saboda ƙwarewarsa a haddar Al-kur’ani.
Malam Yusuf Ɗan-Birni, ya kyautar da motar ce a taron wa’azin wata-wata da Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’a Wa Iƙamatis Sunna (JIBWIS) ta shirya a garin Kubwa da ke yankin Babban Birnin Tarayya.
Malam Yusuf Ɗan-Birni wanda ke sana’ar gyaran waya, ya bai wa jama’a mamaki a yayin da ake tsaka da karatun da misalin ƙarfe 10 nan dare inda ya miƙa makullan motarsa ga mai gabatar da wa’azin, Sheikh Mahmud Assalafi, ya sanar da shi cewa ya kyautar da ita ga majabaƙinsa, Alaramma Usman Nasidi Gusau.
Wani ganau mai suna Malam Nuhu Abu-Huzaifa ya shaida wa Aminiya cewa, wanda ya kyautar da motar na zaune a kusa da shi, sai ya lura yana zubar da ƙwalla a lokacin da alaramman ke karanta Alƙur’ani Mai Tsarki.
Malam Nuhu ya bayyana cewa, “Malami mai fassara Sheikh Mahmud Assalafi ya yi ta yawatawa da alaramman a cikin ayoyi da surorin Wlqur’ani ta hanyan ƙidayo masa surorin da kuma ayoyin, a inda alaramman ke gano su nan take a cikin sauki.”
Ya ce bayan kammala wa’azin da misalin ƙarfe 11 na dare ya ga wanda ya yi kyautar motar ya tsayar da ɗan acaɓa zai hau da nufin komawa gida.
Ya yi addu’ar Allah Ya daɗaɗa wa Yusuf Ɗan-Birni da iyalansa kamar yadda ya daɗaɗa wa Alaramman, Ya kuma maye masa gurbin motar da ya kyautar da wadda ta fita ta.
A zantawarsa da Aminiya a kan lamarin, Babban Limamin Masallacin Badar da ke Garin na Kubwa inda taron ya gudana, sheikh Abdulmumini Ahmad Khalid, ya nuna farin ciki a kan lamarin tare da bayyana kyautar a matsayin abin da ba kasafai yake faruwa ba.
Ya ce, ba a fi wata guda ba, Dan-Birni ya zo da motar da ya saya ƙirar Fijo 406, cewa ya saye ta domin zirga-zirga da na’urorin daukar karatu a bidiyo da sauran ayyukan masallacin, da yake watsawa ta dandalin sada zumunta.
Ya yi addu’ar Allah Ya saka masa da mafi alheri.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Al Ƙurani Alaramma ya kyautar da
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
A ranar Juma’a da yamma, wasu ƴan bindiga ɗauke da makamai sun tare motar haya a mararrabar Ogbabo, kan titin Itobe-Anyigba a jihar Kogi, inda suka yi awon gaba da fasinjoji 9. Direban motar da wasu fasinjoji 6 kuwa sun tsere ba tare da an sace su ba.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:20 na yamma a yankin ƙaramar hukumar Ofu, lokacin da ƴan bindigar suka fito daga daji suka tare titin. Sun tilasta direban motar Toyota mai ɗauke da fasinjoji tsayawa, sannan suka yi harbi cikin iska domin tsoratar da mutane. Direban motar, Sunday Okechi, ya yi dabara ya tsere tare da wasu fasinjoji 6, yayin da sauran 9 suka faɗa hannun ƴan bindigar da suka tafi da su cikin daji.
’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A KoginNisan wurin da aka sace fasinjojin ya yi kusan mita 300 kacal daga shingen Sojoji na irin Ogbabo-Ochadamu. Jami’an tsaro sun isa wurin cikin gaggawa, inda suka tarar da motar haya mai lambar ENZ-55 XS da wata Toyota Carina ‘E’ a ajiye. An fara aikin ceto tare da haɗin gwuiwar ƴansanda, da Sojoji, da ƴan sa-kai da mafarauta domin gano masu laifin da kuma kuɓutar da waɗanda aka sace.
Kakakin rundunar ƴansanda jihar, SP Williams Ovye Aya, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran jami’an tsaro don ceto mutanen da aka sace tare da kama waɗanda suka aikata laifin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp