Aminiya:
2025-10-13@18:09:49 GMT

Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno

Published: 10th, August 2025 GMT

Hukumar Shari’a ta Jihar Borno ta ƙara wa ma’aikatanta 97 girma bayan wani taro na kwanaki huɗu da ta gudanar a Maiduguri.

Muƙaddashin sakataren hukumar, Saleh Khala Jidda ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa cewa ma’aikatan sun samu ƙarin girma ne saboda ƙwazonsu.

EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo  ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato

Waɗanda abin ya shafa sun hada da Majistare 10 daga matakin Majistare mataki na ɗaya zuwa Babban Majistare mataki na biyu.

Sai Majistare daga matakin farko zuwa Babban Majistare na biyu.

Sauran sun haɗa manyan Magatakarda daga mataki na ɗaya zuwa na biyu.

Sai dai a gefe guda, hukumar ta ɗauki mataki kan wani alƙalin Babban Kotun Majistare ta 4 da ke Wulari, Maiduguri, mai suna Yusuf Garba.

Binciken da kwamitin ƙorafe-ƙorafen jama’a ya gudanar ya gano cewa alƙalin ya karkatar da kuɗaɗen shiga na gwamnati har Naira 100,000.

Saboda haka aka sauke shi daga muƙaminsa tare da umartar ya kai rahoto ga Babban Magatakarda domin a sake masa muƙami.

Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa tana da niyyar ci gaba da tabbatar da gaskiya da adalci a kotuna.

Sannan ta ce za ta ladabtar da masu cin hanci da rashawa da kuma girmama masu gaskiya da riƙon amana.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙarin girma Shari a

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Tsaro ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta October 11, 2025 Tsaro Sojoji Sun Ƙaryata Rahoton Cewa Ƴan Bindiga Sun Mamaye Sansaninsu A Kwara October 5, 2025 Tsaro Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ October 4, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Sharhi: Lai Qingde Ba Zai Iya Jirkita Gaskiya Ba
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Yadda Ake Gurasa Ta Semovita
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Venezuala Ta Bukaci Kwamitin Sulhun M.D.D Da Ya Tabbatar Da Cewa: Amurka Tana Barazana Ga Zaman Lafiya