Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna ta shawarci maniyyata aikin Hajjin shekarar 2026 da su fara shirin biyan kudaden ajiya.

Kiran ya biyo bayan taron da Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta gudanar tare da hukumomin Alhazai na jihohi, inda aka bayar da shawarar ajiyar naira miliyan 8 da rabi ga masu niyyar zuwa aikin Hajji, kafin a sanar da hakikanin kudin aikin Hajjin shekarar 2026.

A cikin wata sanarwa, mai magana da yawun hukumar, Yunusa Mohammed Abdullahi, ya shawarci wadanda ba su da fasfo da su gaggauta zuwa Hukumar Shige da Fice ta Kasa domin yin nasu, yana mai cewa shi ne ake amfani da shi wajen hada takardun tafiya.

Najeriya ta sake samun kujeru 95,000 daga Masarautar Saudiyya domin aikin Hajjin 2026, ana kuma sa ran  jihar Kaduna za ta sake samun yawan kujerun da aka saba bata.

Yunusa Mohammed ya kuma bayyana cewa hukumar za ta sanar da maniyyata lokacin da za a fara yin rajista a Jihar Kaduna.

 

Safiyah Abdulkadir 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo

An shawarci sabbin mataimaka na musamman da su kasance masu adalci da gaskiya wajen aiwatar da ayyukansu a ƙaramar hukumar Auyo ta jihar Jigawa.

Shugaban ƙaramar hukumar Auyo, Alhaji Binyaminu Ahmad Adamu Kafur ne ya bayar da wannan shawara yayin bikin rantsar da sabbin mataimaka na musamman 69 da aka gudanar a Auyo.

Alhaji Binyaminu Kafur ya sake tabbatar da kudirin majalisar wajen yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin samar da kayayyaki more rayuwa, don tabbatar da ganin kowa ya  amfana da mulkin dimokuraɗiyya.

Ya yi kira ga jama’a da kada su gaji wajen yin addu’a domin samun nasarar shugabanni wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwarsu.

Shi ma a nasa jawabin, Alhaji Umar Jura ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar bisa zabar mutanen da suka dace don yin aiki a lokacin mulkinsa.

Ya yi kira ga waɗanda aka naɗa da su bada haɗin kai tare da yin aiki tukuru don nuna amincewar da aka nuna gare su.

A madadin waɗanda aka naɗa, Malam Yakubu Muhammad Auyo da tsohon shugaban rikon ƙwarya Mika’ila Auyo sun gode wa shugaban ƙaramar hukumar bisa amincewa da su don yin wannan aiki.

Haka kuma sha alwashin haɗin kai domin cimma manufofin da aka sanya a gaba.

 

Usman Muhammad Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
  • Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
  • Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi
  • Za a biya ma’aikata 445 garatitun sama da biliyan ɗaya a Kebbi
  • Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja
  • Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza
  • An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo