Leadership News Hausa:
2025-08-11@19:32:39 GMT

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Published: 11th, August 2025 GMT

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Rikicin filin gona ya yi sanadin mutuwar mutum biyu tare da jikkata wasu biyu a ƙaramar hukumar Gulani da ke Jihar Yobe. Lamarin ya faru ne a daren Asabar bayan ce-ce-ku-ce tsakanin mazauna ƙauyukan Zango da Azere, waɗanda ke tsakanin iyakokin Gujba da Gulani.

Kakakin rundunar ƴansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya bayyana cewa shalƙwatar ƴansanda ta Bara ta samu kiran gaggawa daga shugaban ƙauyen Zango a ranar 9 ga Agusta, 2025, da misalin ƙarfe 11:30 na dare, inda ya sanar da cewa wasu ƴan daba daga ƙauyen Azere sun kai mummunan farmaki kan manoma.

Gwamnatin Yobe Za Ta Yi Taron Girmama Ɗalibar Turanci Ta Duniya, Nafisa Abdullah Afam Osigwe Ya Zama Sabon Shugaban Kungiyar Lauyoyi Ta Kasa

Wanda aka kashe sun haɗa da Sani Makeri, mai shekara 40, da Abdullahi Maicitta, mai shekara 35, dukkansu ƴan asalin Zango. An garzaya da waɗanda suka jikkata an kai su zuwa babban asibitin Damaturu domin samun kulawa.

SP Dungus ya ce rikicin ya samo asali ne tun bara lokacin damina, duk da ƙoƙarin hukumar ƴansanda wajen sulhu ta hanyar kwamitin daidaita iyakoki na Jiha. Kwamishinan ƴansandan jihar, CP Emmanuel Ado, ya la’anci harin tare da bayar da tabbacin cafke masu laifi, kana ya ja hankalin manoma su guji ɗaukar doka a hannu su kuma nemi sulhu ta hanyar hukumomi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

‘Yansanda sun kama wani da ake zargi da hannu a kisan, mai suna Ahmadu Mairiga, kuma sun ceto shanu 249.

Kwamishinan ‘yansandan Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya ziyarci yankin, ya gana da shugabannin Fulani, sarakuna da shugabannin al’umma, inda ya gargaɗi mazauna yankin da su guji kawo tashin hankali, tare da tabbatar da cewa an ɗauki matakan tsaro don hana sake faruwar irin haka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Gwamnatin Kwara Ta Yi Gargadi Ga Manoman Ruwan Malka Na Wata Agusta
  • Nazari Kan Dalilin Da Ya Sa Kajin Gidan Gona Ke Samar Da Ƙananan Ƙwai 
  • Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
  • Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
  • An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro