Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Published: 10th, August 2025 GMT
Wakilan LEADERSHIP sun lura cewa yanzu ana amfani da wasu daga cikin waɗannan ofisoshin hulɗa da jama’a na Jihar Legas a matsayin matsugunin ‘yan kasuwa na da masu safarar barasa. Binciken da aka yi ya kuma nuna cewa jami’an tsaro da masu kula da waɗannan gidaje suna hayar wasu sassan gine-ginen da daddare don yin haramtattun ayyuka, inda suka mayar da su gidajen karuwai.
Lamarin dai ya haifar da fargaba a tsakanin mazauna yankin da kuma ‘yan kasuwa a yankunan da ke maƙwabtaka da su, inda suka ce ayyukan na da matuƙar haɗari ga tsaro, suna jawo masu aikata laifuka, da kuma zubar da mutuncin wakilan Jihar a Legas.
Lamarin dai ya haifar da fargaba a tsakanin mazauna yankin da kuma ‘yan kasuwa a yankunan da ke makwabtaka da su, inda suka ce ayyukan na da matukar hadari ga tsaro, suna jawo masu aikata laifuka, da kuma zubar da mutuncin wakilan jihar a Legas.
Wakilanmu da suka ziyarci ofisoshin hulɗa da jama’a ga ‘yan iskan gari, sun tabbatar da cewa mutane suna zuwa wurin ba bisa ƙa’ida ba domin neman mafaka tare da biyan masu kula da gidajen kuɗi.
A wasu ofisoshin da akwa na jihohin Arewa, waɗanda ake kasuwanci da su ba bisa ƙa’ida ba ‘yan kasuwa, masu sana’a, da ma’aikatan gine-gine da ke aiki a wurare daban-daban a faɗin Legas. An ba da rahoton cewa jami’an haɗin gwiwar sun canza ofisoshin gudanarwa zuwa abin da suke kira ƙakunan “Arrangee” ko “wurin barci”, da kuma ofisoshin talla da shagunan caca. Waɗanda suka kama hayar wurin ba bisa ƙa’ida ba, maza da mata, sun kuma mayar da ofisoshin gidajen zama.
An ruwaito cewa wasu mutanen ma sun kwaso iyalansu sun zo sun tare a waɗannan gidaje, yayin da tuni wasu ma har sun hayayyafa suna renon ‘ya’yansu a wurin. Yawancin waɗannan tsoffin gine-ginen da ke Ɓictoria Island, yanzu sun lalace, inda ‘yan kama wuri zauna ba bisa ƙa’ida ke aiwatar da haramtattun ayyuka a fili ba tare da takura ba.
LEADERSHIP WEEKEND ta ci gaba da cewa, wasu daga cikin waɗannan gidaje an yi watsi da su gaba ɗaya kuma jihohin da suka mallake su sun yi watsi da su, wanda hakan ya ba da damar ‘yan damfara su gudanar da ayyukansu cikin walwala. Wasu mutane sun canza sassan ofisoshin zuwa wuraren caca, mashaya na gida, gidajen abinci, da kuma abin da ake kira ɗakunan Arrangee da kuma ɗakunan bacci.
Gidajen Jihohin Kwara, Borno, Bauchi, Adamawa, Zamfara, Nasarawa, Gombe, Benue, Kebbi, Imo, Bayelsa, da Ribas na daga cikin waɗanda abin ya shafa. Ziyarar da aka kai wa waɗannan gine-ginen ya nuna cewa yawancin gine-ginen sun lalace, inda jami’an tsaro da ke gadin ginin ke ba da hayar ɗakunan da ke cikin ofisoshin a matsayin ɗakunan yi “barci ka tafi”.
Adamawa
A Jidan Jihar Adamawa, ya yi matuƙar rauni, saboda a hankali sassan ginin ya lalace yana kuma dab da rugujewa idan gwamnatin jihar ba ta sa baki ba. Rahotanni sun bayyana cewa wasu mutane ‘yan Jihar Adamawa ne suka mamaye wasu sassan ginin, inda suka bar shi ba tare da kulawa ba, ƙazanta, sannan tankuna ruwan gidan duk sun farfashe, magudanan ruwa da rufin gidajen duk sun lalace.
Zamfara
Wasu daga cikin ’yan damfara ne a cikin gidan Jihar Zamfara da ke kan titin Adeola Odeku, Ɓictoria Island, inda suka ce suna zaune ne a ginin ne saboda kusancinsa da wuraren aikinsu. Nau’in mtanen da ke cikin gidan dai direbobi ne da kuma masu aikin shara.
Binuwe
Wani bincike da wakilinmu ya yi ya gano cewa an bayar da hayar gidan Binuwe da ke Legas inda a yanzu otal ne na Presken tun daga shekarar 2020. Presken ya karɓe ofishin inda ya mayar da shi otal, da wurin sayar da barasa.
Kuɗin ɗakunan da ke ofishin Liaison Office na Binuwe, wanda yanzu haka Presken Hotels and Resorts Limited ke gudanarwa, ya fara daga Naira 56,000 zuwa Naira 153,000, gwargwadon girman ɗakunan.
Kwara
A gidan Jihar Kwara, wani jami’an tsaro da wakilinmu ya gana da shi, ya ce a yanzu an hana ba da wurin baccin yi ka tafi, an gama gyara wurin. Da aka ci gaba da bincike, sai aka gani cewa iyalai da dama, galibinsu Fulani Musulmi, a halin yanzu suke zaune a ofisoshin na Jihar Kwara, inda suke fakewa a can.
Ya musanta duk wani shiri da gwamnati ta yi na sayar da kadarorin amma ya yarda cewa ana ƙoƙarin gyara ginin, tare da shirin fara aiki nan ba da daɗewa ba.
Nasarawa
A Ofisoshin Nasarawa, wasu Hausawa ne da fulani ke zaune a ciki, yayin da masu sana’ar hannu, kamfanin lotto, da masu sana’ar Betnaija suka kama suna gudanar da harkokin kasuwanci a harabar.
Jihohin Ribas Da Bayelsa
Ga Ofisoshin Jihar Ribas da Bayelsa, duk da cewa suna yanki guda a fannin gudanarwa kuma ofisoshinsu na aiki ɗaya, jami’an tsaron da ke ƙofar gidan su kan yi sulhu ta hanyar karɓar kuɗi daga hannun mutane tare da ba wa masu kwana ɗaki don samar wa kansu kuɗaɗen shiga. Ɗaya daga cikin jami’an tsaro na ofishin jihohin Bayelsa da Ribas ya ce, “Mu jami’an tsaro ne guda uku da ke bakin aiki, duk wanda ya ke son ya biya ya yi ajiya sai ya sasanta da mu uku kafin mu ba shi ɗakin su kwana.
Filato
Binciken da aka gudanar a ofishin Jihar Filato da ke kan titin Ahmadu Bello a Legas, ya nuna cewa ofishin a yanzu ya zama wani sansanin wucin gadi da ke dauke da wasu ‘yan tsiraru kamar sansanin ‘yan gudun hijira, inda ake saukar ‘yan gudun hijira.
Bauchi da Gombe
Ga ofishin Jihohin Bauchi da Gombe da ke Legas, binciken da wakilinmu ya gudanar, ya zanta da ɗaya daga cikin jami’an tsaro mai suna Isiaka, inda ya bayyana cewa, suna da hannu dumu-dumu a cikin sa-in-sa da ake yi a ɗakin da ake kira ‘arrangee’, inda mutane za su riƙa kawo mata karuwai.
Ya ce kuɗin hayar ya fara ne daga Naira 4,000 zuwa Naira 15,000 a ɗakuna “baccin yi ka tafi”.
Gidan Jihar Bauchi ya zama cikakken sansanin ‘yan gudun hijira a Legas, inda ake tsugunar da mutane iri-iri da suka hada da ‘yan gudun hijira da kuma waɗanda ke fuskantar matsalar masauki. Su kan kafa tanti na wucin gadi, suna shimfiɗa don su rufa wa kansu asiri idan sun yi barci. Isiaka ya shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa, “Muna da ɗakunan Naira 7,000, Naira 8,000, Naira 10,000, da kuma Naira 15,000, amma ba mu da ruwa ko banɗaki ga duk wanda zai kwana a nan, sai dai idan ka je banɗaki da ɗakin wanka da ke kusa da kai.”
Kano Da Sakkwato
Dangane da Ofisoshin Kano da Sakkwato kuwa, suna da ɗimbin jama’a, galibinsu masu yankan farce ne da masu sayar da abinci, da masu sana’ar hannu waɗanda suka mamaye kewaye da gaban ofishin.
Abia
Dangane da ofishin jihar Abia kuwa, jami’in tsaron da ya bayyana sunansa da Hosea Alli ya shaida wa LEADERSHIP Weekend cewa yana karɓar Naira 20,000 na wani ɗakin kwana da ke cikin ofishin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yan gudun hijira jami an tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
“Abin takaici ne ace Nijeriya tana karancin Mlaman makaranta da suka kai 194,876 a makarantun gwamnati a fadin tarayyar Nijeriya. Halin da makarantunmu na Sakandare suke ciki shi ma lamarin bata canza zane ba. Rashin isassun Malamai shi ma lamarin abin damuwa ne domin kuwa sannu a hankali hakan zai iya shafi samar da ingantaccen ilimi a makarantunmu kamar yadda sakamakon hakan ba zai haifar da da mai ido ba cewar, Amba”.
Don haka ya ja kunnen Nijeriya cewa rashin isassun Malaman zai iya kawo cikas wajen kokarin da Nijeriya ta ke yi na cimma muradin ci gaba na 4 (SDG 4) da ya kunshi ingantaccen ilimi ba tare da wani bambanci ba, tsakanin gwamnatoci uku ba tare da wani bata lokaci ba a dauki mataki wanda ya dace.
Ya ci gaba da bayanin“Mu ma mun sa bakinmu wajen kira da babbar murya domin aikin koyarwa ya kasance abinda kowa yake sha’awar yi ne ga matasa masu tasowa. Dole ne gwamnati ta dauki yawan Malaman da suka kamata a dauka tare da yin la’akari da ingancinsu, domin a ci gaba da samar da ingantaccen ilimi a tsarin tafiyar da makarantunmu,”.
Duk alkawarin da aka yi na jin dadin Malaman makaranta ba a cika shi
Amba har ila yau nya nuna rashin jin sadinsa kan yadda aka kasa cika alkawuran jin dadin da aka yi wa Malaman makaranta’, duk kua da yake an yi alkawarin tun, a shekarar 2020. Yana iya tunawa zamanini mulkin tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya amince da wasu abubuwan da za su taimaka wadanda suka hada da tsarin albashi na musamman, da kuma irin lokacin da za su yi ritaya, da gidaje masu saukin kama haya a kauyuka amma suma ba a kai ga yinsu ba.
“Abin takaici ne cewar bayan lamarin shekarun da za’ayi ritaya daga aiki idan an kai an gabatar dasu, 65, abinda Jihohi 22 da Babban Birnin Tarayya Abuja, yawancin duk abubuwan da aka amince za ayi masu har yanzu ba a cika alkawarin ba. Muna kiran gwamnatin tarayya da Jihohi su cika dukkan aalkawuran za aka yi na game da jin dadin Malaman makarabta kamar yadda suke, saboda a samu damar dawo da irin martabar da aka san aikin koyarwa yana da ita kamar yadda ya ce,”.
Game da aiwatar da dolar mafi karancin albashi na kasa kamar yadda aka amince a shekarar 2024, Shugaban kungiyar Malamai ta kasa yace Jihohi goma basu cika ka’idar ba kamar yadda take ba, ta aiyatar da mafi karancin albashi, yayin da Jihohi hudu ma basu fara biya ba.
Kungiyar Malaman ta yi magana kan rashin ba shi bangaren ilimi kuaddaen da suka dace a bashi, inda suka ce Nijeriya ta ci gaba da kasancewa a baya kan yadda mizani na kasa da kasa wato shawarar da aka yanke na kason da aka amincewa bangaren ilimi, inda aka ce a rika ware ma shi bangaren kashi 4–6 na kudaden da suk shigo ma kasa a duk shekara GDP oko kuma 15–20 na gaba dayan kasafin kudin zuwa ga bangaren ilimi.
Amba ya ce ya zuwa wayan Maris na shekarar 2024, kamar Naira biliyan 54 da aka ware ma bangaren ilimin bai daya (UBE) har yanzu ba a samu amsar ko kwabo ba saboda rashin bada kaso da akace a rika badawa wato Jihohi da Babban Birnin Tarayya Abuja.
“Rashin yadda Jihohi suka ki biyan kason na sun a kudi kaman a kai ga basu tallafin na UBEC, hakan ya kara gurgunta rashin bunkasa ilimin na bai daya, da kuma taimakawa tsare= tsaren da za su jawo hankalin Malamai ya raja’a kan aikin koyarwa kamar yadda ya ce,”.
Hakanan ma kungiyar bata ji dadin da wani kokarin na gwamnatin Jihar Edo ban a ta mika wasu makarantun gwamnati ga Hukumomi da ba nata ba, da kuma kungoyoyi masu zaman kansu, abinda ta kalla a matsayin wasu matakai ne da za su kawo cikas wajen cimma burin samar da ilimi kyauta.
Kungiyar ta ce wadannan matakan suna kawo barazana wajen samar da adalci, musamman ma ga irin wadanda basu da halin ba ‘ya’yan nasu ilimi, kamar ‘yanmata, yara masu kulawa ta musamman, da kuma wadanda suke can kauyuka.
Ta yi kira da gwamnatin Jihar Edo ta daukai matakan da suka kamata kamar yadda tsarin mulki ya tanadar wajen samar da ilimi kamar yadda lamarin yake yadda doka ta tanadar.
Kungiyar ta yi magana ne kan muhimmancin kulawa jin dadin Malamai,inda ta yi tunatarwa da rahoton shekarar 2008 kan kungiyar ma’aikata ta duniya da kuma hukumar ILO/UNESCO, in da aka yi bayanai kan muhimmancin jin dadin Malamai ’ a matsayin irin abubuwan da suke jan mutane na sha’awar aikin koyarwa da kuma ci gaba da zaman kwararrun a makarantu.
Mr. Bobby Winful na Kwalejin gwamnatrin tarayya ta maza da je Abuja Abuja, ya dora alhakin rashin Malamai kan wadansu abubuwa, da suka hada da rashin kulawa dajin dadin Malamai, da kuma karancin Malaman d aka amince da su masu lasin na aikin koyarwa.
“Muna karancin Malamai ne saboda yadda ba a kulawa da hakkin Malamai bare jin dadinsu abin ba wani abin azo a gani bane. Sau da yawa wasu wuraren ba ma a biyan albashin. Abin mamaki ace wai wasu Malaman suna zuwa aiki har tsawon shekara uku ba tare da albashi ba. Hakan shi yasa ake samun raguwar Malamai masu takardar shedar da aka amince sun cancanta su koyar, saboda yawancin dalibai a Jami’a basu sha’wara karanta darasin ilimi, duk wannan ba domin komai ba saboda babu wasu abubuwan da za su ja hankali a sharuddana aikin nasu, ba wata maganar jin dadinsu da kuma ,aganar albashi kamar yadda ya yi karin bayani,”.
Shugabar makarantun Chalcedony, Dakta. Mary Chinwuba, ta bayyana babban dalilin da ya kawo karancin Malamai a Nijeriya saboda babu wasu abubuwan jan hankali daga cikin sharuddan aikinsu ba, don haka ta yi kiran da ayi gaggawar inganta sharuddan aikinsu da kuma jin dadinsu.
Gwamnati ta yi kira ga Malaman makaranta da su hada kansu
A na shi jawabin Minisatan ilim, Dakta. Maruf Olatunji Alausa, ya kara jaddada manufar gwamnati ta sanin cewa Malamiai sune babban tubali wajen gina kasa da ci gabantar.
Ya yi karin haske “Malamai sune ginshikin ci gaban al’umma hakanan kuma babbar hanyar bi zuwa wajen bunkasa al’umma da kuma kasa.Don haka idan an yiwa Malamai wani ihisani hakan baya nuna ta hakan ne aka san da su ba, manufa kuwa sun kasance tamkar zuba jari ne domin samun ingantaccen ilimi, karuwar da dalibi zai yi, da kuma yadda kasa za ta kasance cewar Dakta Alausa.
Dakta Alausa ya bayyana hanyoyi masu yawa domin inganta shi aikin koyarwar wadanda suka hada da, tsarin ilimin Malami na kasa, tsarin sa ido na hukumar al’amuran Malamai, ci gaban bunkasa kwarewar aikin Malamta na NTI, da kuma irin yadda hukumar ilimin bai daya take taimakawa shi bangaren na ilimi.
An karrama Gwamnoni hudu saboda inganta jin dadin Malaman makaranta’
An karrama gwamnoni hudu saboda yadda suke taimakawa harkar ilimi ya wuce duk irin tunanin da mutum zai yi, saboda bunkasa jin dadin Malamai da yadda lkamarin ilimi yake a Jihohin nasu.
An yi bikin karramar ne, a Eagle Skuare, Abuja, gwamnonin da aka karrama sun hada da Katsina, Adamawa, Kogi, da kuma Delta saboda tsare-tsaren da suka bullo da su wadanda za su karawa Malamai kwarin ne su rungumi aikin nasu da gaskiya, da kuma gyara hanyoyin da ake amfani da su wajen koyarwa ko kuma a takaice yanayin da yafi dacewa da koyarwa da koyo.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA