Aminiya:
2025-11-08@18:29:11 GMT

Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno

Published: 8th, August 2025 GMT

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF), ta kai hare-hare ta sama a yankin Rann, wani gari da ke Jihar Borno, wanda ake zargin ya zama mafakar ’yan ta’adda.

Wannan aiki na cikin shirin Operation Haɗin Kai, kuma ya yi sanadin hallaka ’yan ta’adda da dama.

’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa ’yan ta’addan sun fara guduws bayan yunƙurinsu na kai hari sansanin sojoji ya ci tura.

Da suka hangi jiragen yaƙi na sojojin sama, sai suka fara tserewa daga maɓoyarsu, amma an kashe da yawa daga cikinsu ta hanyar ɓarin wuta.

Wani mazaunin Rann ya ce da farko sun yi zaton cewa ’yan ta’addan ne za su kai musu hari saboda ƙarar da suka ji kamar ta bindiga.

Daga baya ne suka fahimci cewa sojoji ne ke gudanar da aiki.

Mai magana da yawun Rundunar Sojin Sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya tabbatar da harin a cikin wata sanarwa.

Ya ce sun samu bayanan sirri da suka tabbatar da inda ’yan ta’addan suke, kuma bayan sojojin ƙasa sun gano su suna guduwa, sai aka aike jiragen yaƙi da suka kai musu farmaki.

Harin ya daƙile barazanar ’yan ta’addan, kuma ya dawo da zaman lafiya a yankin.

Ejodame, ya ƙara da cewa wannan aiki ya nuna irin sadaukarwar da Rundunar Sojin Sama ke yi wajen kare dakarunta da kuma daƙile duk wata barazanar ’yan ta’adda.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda hari yan ta addan yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita

Wasu fusatattun matasa a ƙauyen Sokupkpan da ke karamar hukumar Edu a jihar Kwara, sun kashe Babban Limamin yankin, Mallam Abdullahi Audu, bisa zargin shi da alhaki kan mutuwar wani matashi, Ibrahim Gana ta hanyar maita.

Shaidu sun ce lamarin da ya faru a ranar Laraba ya jefa al’ummar yankin cikin rudani da firgici.

Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa Za a gudanar da wasannin ƙwallon yashi a Abuja

An ce wannan farmakin ya samo asali ne daga zargin cewa limamin ya yi amfani da maita wajen cutar da mamacin.

A cewar majiyoyi, kafin rasuwarsa, Gana ya dade yana fama da wata cuta da ba a bayyana ba, kuma ya sha faɗa cewa Babban Limamin yana damunsa a mafarki.

An ce ya sha gaya wa abokai da danginsa cewa limamin ne ke haddasa tabarbarewar lafiyarsa ta hanyar sihiri.

“Yayin da lafiyarsa ke ƙara tabarbarewa, mutane suka fara yarda da zargin nasa. Da ya mutu, wasu matasa suka yanke shawarar cewa limamin ne ke da laifi,” in ji wata majiya daga yankin.

A ranar Laraba, rikici ya ƙara ƙamari yayin da ’yan uwan mamacin – Mohammed Shaba, Mamudu Gana, da Ndakpotun Issa, suka tara wasu matasa don tunkarar limamin.

Duk da ƙoƙarin wasu dattawa na kwantar da hankali, gungun matasan sun kai wa limamin hari, inda suka lakada masa duka har ya ce ga garinku nan.

“Sun afka wa limamin suna zarginsa da kashe Gana ta hanyar sihiri. Sun ƙi sauraron duk wanda ya yi ƙoƙarin dakatar da su,” in ji wata majiyar.

’Yan sanda daga ofishinsu na Tsaragi sun isa yankin bayan faruwar lamarin, inda suka kama wasu da ake zargi da jagorancin harin.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar Kwara, SP Adetoun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis, tana mai bayyana shi a matsayin “kisan gilla mai ban tsoro.”

Ta ce binciken farko ya nuna cewa bayan mutuwar Gana mai shekaru 25 a ranar 4 ga watan Nuwamba, ’yan uwansa Mohammed Shaba da Mahmud Gana sun zargi Babban Limamin da haddasa mutuwarsa, kuma suka tara wasu don kashe shi.

A cewarta, “An kama mutane huɗu, kuma ana ci gaba da ƙoƙarin kama sauran da suka shiga lamarin.”

Ta ce Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Adekimi Ojo, ya yi alla-wadai da lamarin, yana mai gargaɗin jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

Tuni da aka yi jana’izar limamin bisa koyarwar addinin Musulunci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Hamas Ta Goyi Bayan Matakin shari’ar Turkiyya Kan Neman kama Masu Take Hakkin Bil’Adama A Isra’ila
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Ɗan shekara 2 ya rasu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800
  • Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar
  • An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai