Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno
Published: 8th, August 2025 GMT
Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF), ta kai hare-hare ta sama a yankin Rann, wani gari da ke Jihar Borno, wanda ake zargin ya zama mafakar ’yan ta’adda.
Wannan aiki na cikin shirin Operation Haɗin Kai, kuma ya yi sanadin hallaka ’yan ta’adda da dama.
’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa ’yan ta’addan sun fara guduws bayan yunƙurinsu na kai hari sansanin sojoji ya ci tura.
Da suka hangi jiragen yaƙi na sojojin sama, sai suka fara tserewa daga maɓoyarsu, amma an kashe da yawa daga cikinsu ta hanyar ɓarin wuta.
Wani mazaunin Rann ya ce da farko sun yi zaton cewa ’yan ta’addan ne za su kai musu hari saboda ƙarar da suka ji kamar ta bindiga.
Daga baya ne suka fahimci cewa sojoji ne ke gudanar da aiki.
Mai magana da yawun Rundunar Sojin Sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya tabbatar da harin a cikin wata sanarwa.
Ya ce sun samu bayanan sirri da suka tabbatar da inda ’yan ta’addan suke, kuma bayan sojojin ƙasa sun gano su suna guduwa, sai aka aike jiragen yaƙi da suka kai musu farmaki.
Harin ya daƙile barazanar ’yan ta’addan, kuma ya dawo da zaman lafiya a yankin.
Ejodame, ya ƙara da cewa wannan aiki ya nuna irin sadaukarwar da Rundunar Sojin Sama ke yi wajen kare dakarunta da kuma daƙile duk wata barazanar ’yan ta’adda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda hari yan ta addan yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gargaɗi maƙarrabansa cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin da aka ɗora masa, ya yi murabus.
Wannan gargaɗi na zuwa ne bayan murabus ɗin Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi, ya yi biyo bayan belin wani da ake zargin dilan miyagun ƙwayoyi, Sulaiman Danwawu.
Manoma sun koka kan rabon takin gwamnati a Sakkwato Hatsarin Mota: Yadda hanyar Lambata ke laƙume rayuka a NejaWannan lamari ya tayar da ƙura, wanda hakan ya sa Gwamna Abba, ya ɗauki mataki.
A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, gwamnan ya bayyana rashin jin daɗinsa kan lamarin.
Hakan ta sa ya jaddada buƙatar dukkanin mambobin majalisar da sauran manyan jami’an gwamnati su kasance masu gaskiya da riƙon amana.
“Ba za mu lamunci kowace irin ɗabi’a ta ƙashin kai da za ta ci gaba da lalata ƙimar gwamnatinmu ba,” in ji Gwamnan.
“Dukkanin ma’aikata dole su kasance masu lura da kuma ɗaukar nauyin ayyukansu. Ba ofishinku kawai kuke wakilta ba, kuna wakiltar gwamnatinmu.”
Gwamnan ya ƙara da cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin amanar da aka ɗora masa ba, ya yi murabus da kansa maimakon aikata wani abu da zai ɓata sunan gwamnati.
Ya kuma nanata cewa yaƙi da miyagun ƙwayoyi da sauran munanan ɗabi’u a cikin al’umma yana daga cikin ginshiƙin mulkinsa.
Ya ce duk wanda aka samu yana da hannu kai-tsaye ko a kaikaice wajen taimaka wa masu aikata irin waɗannan laifuka, zai fuskanci hukunci.
“Mun hau mulki da kyakkyawan manufa ta daidaita al’amura, gaskiya da ci gaba a Jihar Kano. Wannan buri ba zai taɓa taɓewa ba,” in ji shi.
Wannan mataki da gwamnan ya ɗauka na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ke ƙara barazana ga matasa da zaman lafiyar al’umma a jihar.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da adalci, gaskiya da kyakkyawan shugabanci ga al’ummar Jihar Kano.