Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@03:39:33 GMT

BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano

Published: 18th, April 2025 GMT

BUK Ta Shirya Taron Na Shekara-shekara Akan Malam Aminu Kano

Cibiyar Nazarin Dimokuradiyya ta Aminu Kano a Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta shirya taron shekara-shekara karo na 23 don tunawa da cika shekaru 42 da rasuwar Malam Aminu Kano.

 

 

A nasa jawabin, Shugaban jami’ar Bayero, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya jaddada muhimmancin taron shekara-shekara wajen kiyaye manufofin da Malam Aminu Kano ya tsaya a kai.

 

Farfesa Haruna Musa wanda mataimakin shugaban jami’ar kula da harkokin ilimi ya wakilta, ya bayyana cewa jerin laccoci an yi niyya ne don ba da damar fahimtar juna dangane da yanayin tarihi.

 

“A ci gaba da kokarin da jami’ar mu ke yi na karfafa al’adun dimokuradiyyar Najeriya, muna gayyatar manyan mutane duk shekara don gabatar da laccoci a gidan Mambayya kan batutuwan da suka shafi kasa baki daya.

 

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, ya bayyana Malam Aminu Kano a matsayin wani hamshakin mai neman sauyi na Afirka, kuma dan gwagwarmayar siyasa mai jajircewa, wanda rayuwarsa ke ci gaba da zaburar da al’umma.

 

 

Wanda ya samu wakilcin mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdulsalam Gwarzo, ya jaddada cewa taken taron ya dace saboda halin da kasar nan ke ciki.

 

A nasa jawabin, Farfesa Kabiru Isa Dandago ya gabatar da kasida mai taken “Siyasar Gyaran Haraji a Najeriya: Tsammani da Gaskiya.

 

Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa taron tunawa da marigayin ya hada masana, masana siyasa, da shugabannin kungiyoyin farar hula, inda suka yi bita a kan rayuwar marigayi dan kishin kasa, malami, dan juyin juya hali.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa za ta ci gaba da shirin gudanar da babban taronta wanda za a yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba a Ibadan da ke Jihar Oyo.

Tun da farko, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana jam’iyyar gudanar da taron, inda ta ce PDP ta karya dokokinta na cikin gida.

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP

Mai shari’a James Omotosho, wanda ya jagoranci shari’ar, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da kada ta karɓi ko ta wallafa sakamakon taron har sai PDP ta cika dukkanin sharuɗan da doka ta tanada.

Sai dai a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar da yammacin ranar Juma’a, kakakinta na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce jam’iyyar ba za ta dakatar da shirin gudanar da taron ba.

Ya bayyana hukuncin kotun a matsayin tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Najeriya.

Ologunagba, ya ce hukuncin ba zai hana PDP ci gaba da shirye-shiryenta na zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa ba.

Ya yi nuni da cewa Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa jam’iyyu na da ’yancin tafiyar da harkokinsu na cikin gida.

“PDP na kira ga mambobinta da shugabanni a faɗin ƙasar nan da su kuma ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa jam’iyyar mai bin doka ce, kuma ta umarci lauyoyinta da su ɗaukaka ƙara game da hukuncin kotun.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma