Majalisar Dokokin Kano Ta Karɓi Ƙarin Kasafin Kuɗi Na 2025
Published: 11th, August 2025 GMT
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta karɓi ƙarin kasafin kuɗi na shekarar 2025 daga bangaren zartarwa na jihar domin tattaunawa da amincewa.
Bisa wasikar da bangaren zartarwa ya aika wa Majalisar, ana neman amincewar ta kan ƙarin kasafin kuɗi na kimanin Naira biliyan 170 domin aiwatar da muhimman ayyukan ci gaba a fadin jihar.
Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya bayyana cewa bangaren zartarwa yana neman wannan ƙarin kuɗi ne domin gudanar da ingantattun ayyuka da za su amfani rayuwar al’ummar jihar.
Bayan tattaunawa, ‘yan majalisar sun mika kudirin ga Kwamitin Majalisa kan Kasafin Kuɗi domin yin bincike da shirye-shiryen aiwatar da dokokin da suka dace.
A wani labarin kuma, majalisar ta karɓi wasika daga bangaren zartarwa mai ɗauke da sunan Barrista Saidu Yahaya a matsayin sabon Shugaban Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano (PCACC).
Nadin nasa ya biyo bayan karewar wa’adin tsohon shugaban hukumar, Barrista Muhyi Magaji Rimin Gado.
An mika sunan sabon shugaban zuwa ga Kwamitin Majalisa kan Ƙorafe-ƙorafe domin ci gaba da tantancewa da gudanar da matakan doka.
Majalisar ta dage zaman ta zuwa washegari Talata 12 ga watan Agustan 2025.
Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: bangaren zartarwa
এছাড়াও পড়ুন:
Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina
Kwamishiniyar Ilimi ta Jihar Gombe, Dokta Aishatu Umar Maigari, ta ce talauci da nuna bambanci na daga cikin manyan dalilan da ke hana yara mata damar samun ilimi a jihar.
Ta bayyana hakan ne a wajen bikin Ranar Yara Mata ’Yan Makaranta ta Duniya ta shekarar 2025, wanda Shirin AGILE tare da Access Initiative Africa da Nudge Initiative suka shirya a Gombe.
Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a BornoA wajen bikin, Uwargidan Gwamnan Jihar Gombe, Asma’u Inuwa Yahaya, ta yaba da yadda gwamnatin jihar ke ƙoƙarin tabbatar da cewa ba a bar wata yarinya a baya wajen samun ilimi.
Ta ce Gwamnan jihar, ya bai wa ilimin yara mata muhimmanci, wanda hakan ya sa ake samu ƙaruwa yara mata da ke zuwa makaranta.
Kwamishiniyar, ta ƙara da cewa ma’aikatar ilimi tana aiki wajen samar da sabbin manufofi da tsare-tsare da za su taimaka wajen rage waɗannan matsaloli da tabbatar da damar ilimi ga kowa cikin adalci.
A nata jawabin, Kodinetan Shirin AGILE, Dokta Amina Haruna Abdul, ta ce bikin na bana an shirya shi ne don ƙarfafa gwiwar yara mata wajen ci gaba da neman ilimi duk da ƙalubalen da suke fuskanta.
Ta gode wa Uwargidan Gwamnan da ma’aikatar ilimi bisa goyon bayansu.
Haka kuma, Akawun Majalisar Dokokin Jihar Gombe, Barista Rukayyatu Jalo, ta shawarci yara mata da su dage wajen yin karatu, inda ta bayyana cewa ilimi ne hanyar da za ta gina rayuwarsa.
Wasu daga cikin ɗaliban da suka halarci bikin, sun bayyana farin ciki da godiya kan shirya taron saboda yadda ya ƙara musu ƙwarin gwiwa.
Ɗalibai da dama sun gudanar da muhawara da wasan kwaikwayo a wajen taron.