HausaTv:
2025-05-21@20:29:28 GMT

Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya

Published: 18th, April 2025 GMT

Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, ya yi kakkausar suka dangane da yawaitar kashe-kashen da ake yi a jihar Filato da sauran sassan Arewacin Nijeriya, inda ya dora laifin kitsa tashe-tashen hankula da nufin tada zaune tsaye a Nijeriya.

A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, Fani-Kayode ya yi ikirarin cewa wadanda ke haddasa tashe-tashen hankula ba wai kawai ’yan tada kayar baya ba ne, a’a, wasu ‘yan kasashen waje ne da ake zargin suna shigowa Nijeriya ta kan iyakokin kasar, da nufin raba kan al’ummar kasar ta hanyar addini da kabilanci.

Fani-Kayode ya yi gargadin cewa, rikicin da ake fama da shi na da kamanceceniya da yadda aka kirkiri tashe-tashen hankula a zabukan shekarar 2015, inda tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya fuskanci irin wannan tashin hankali.

“Haka aka shirya a shekarar 2014 kafin a kayar da Goodluck Jonathan, yanzu kuma sun fara shirin irin haka domin tunkarar 2027,” in ji shi. “Mun san su wane ne, kasashen waje ne daga cikinsu har da kasashen Yamma da Isra’ila, da wasu da dama. Ba sa son kwanciyar hankali a Nijeriya.” In ji Femi Fani-Kayode.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Fani Kayode

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Kula da lafiya na nufin yin abubuwa da ke kare mutum daga kamuwa da cututtuka da kuma tabbatar da cewa jiki na aiki yadda ya kamata.

Wannan ya haɗa da cin abinci mai gina jiki, motsa jiki akai-akai, da dai sauran su.

Sai dai a wannan zamani ’yan Najeriya ba kasafai suke kula da lafiyar jikinsu ba, a mafi yawan lokuta ma sai ciwo ya kwantar da mutum sannan yake tunawa da likita.

Ko waɗanne matakai ya kamata al’umma su ringa dauka wajen kare kansu da kuma lafiyar jikinsu?

NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a? DAGA LARABA: Tasirin Mulkin Karɓa-Karɓa A Najeriya

Shirin Najeriya A YAU na wannan lokaci zai yi nazari ne kan yadda al’umma za su dinga kula da lafiyar jikinsu.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
  • Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ba Ta Da Alkiblar Siyasa
  • Wasu Shugabannin Turai Sun Yi Barazanar Ladabtar Da Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Gwamnatin Tarayya Ta Nanata Kudurin Koyawa Matasa Sana’o’in Hannu
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za Ku Kula Da Lafiyar Jikinku
  • Iran Ta Yi Watsi Da Da’awar Kungiyar Hadin Kan Kasashen Larabawa Kan Tsibiran Kasarta
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?