Fani-Kayode ya zargi Isra’ila da Hannu a tashe-tashen hankula a Najeriya
Published: 18th, April 2025 GMT
Tsohon ministan sufurin jiragen sama, Femi Fani-Kayode, ya yi kakkausar suka dangane da yawaitar kashe-kashen da ake yi a jihar Filato da sauran sassan Arewacin Nijeriya, inda ya dora laifin kitsa tashe-tashen hankula da nufin tada zaune tsaye a Nijeriya.
A wani faifan bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta, Fani-Kayode ya yi ikirarin cewa wadanda ke haddasa tashe-tashen hankula ba wai kawai ’yan tada kayar baya ba ne, a’a, wasu ‘yan kasashen waje ne da ake zargin suna shigowa Nijeriya ta kan iyakokin kasar, da nufin raba kan al’ummar kasar ta hanyar addini da kabilanci.
Fani-Kayode ya yi gargadin cewa, rikicin da ake fama da shi na da kamanceceniya da yadda aka kirkiri tashe-tashen hankula a zabukan shekarar 2015, inda tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya fuskanci irin wannan tashin hankali.
“Haka aka shirya a shekarar 2014 kafin a kayar da Goodluck Jonathan, yanzu kuma sun fara shirin irin haka domin tunkarar 2027,” in ji shi. “Mun san su wane ne, kasashen waje ne daga cikinsu har da kasashen Yamma da Isra’ila, da wasu da dama. Ba sa son kwanciyar hankali a Nijeriya.” In ji Femi Fani-Kayode.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Fani Kayode
এছাড়াও পড়ুন:
Kasashen Iran Da Tunusiya Sun Jaddada Karfafa Alaka A Tsakaninsu A Bangarori Da Dama
Ministan harkokin wajen kasar Iran da takwaransa na Tunisiya sun jaddada cewa: Warware matsalar Falasdinu na bukatar kawo karshen mamayar da ake yi
Ministocin harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Tunisiya sun jaddada cewa: Warware matsalar Falastinu na bukatar kawo karshen mamaya da kuma tabbatar da hakkin al’ummar Falastinu na cin gashin kansu.
Wannan dai na zuwa ne a yayin ganawar da ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Abbas Araqchi da ministan harkokin wajen kasar Tunisiya Mohamed Ali Nafti suka yi a ranar Laraba a gefen taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar ‘yan ba ruwan mu ta NAM karo na 19 a birnin Kampala na kasar Uganda.
A yayin wannan ganawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan ci gaban da aka samu a dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, da suka hada da shirye-shiryen taron hukumar tattalin arziki ta hadin gwiwa, tare da tabbatar da aniyar kasashen biyu na karfafa alaka da hadin gwiwa a dukkan fannoni.
Har ila yau, sun yi musayar ra’ayi kan abubuwan da ke faruwa a yankin yammacin Asiya da kuma mamaye Falastinu bisa fahimtar da aka cimma a Masar na dakatar da kisan kare dangi. Sun jaddada nauyin da ke wuyan kasashen da ke ba da tabbacin hana yahudawan sahayoniyya karya yarjejeniyar da aka cimma.
An jaddada cewa warware matsalar Falastinu na bukatar kawo karshen mamayar da ake yi da kuma tabbatar da hakkin al’ummar Falastinu na cin gashin kansu, sannan kuma wajibi ne a bin doka da oda da kuma wajibi kasashe su goyi bayan al’ummar Falastinu wajen aiwatar da wannan muhimmin hakki da ‘yantar da kansu daga mamaya da kuma kangin fuskantar nuna wariyar al’umma da kuma mulkin mallaka.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Afirka Ta Kudu Ta Jaddada Aniyarta Ta Ci Gaba Da Shari’ar Neman Hukunta Isra’ila Kan Batun Gaza October 16, 2025 Gwamnatin Kamaru Ta Gargadi Dan Takarar Da Ya Shelanta Kansa A Matsayin Wanda Ya Lashe Zabe October 16, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar NAM Sun Nuna Goyon Bayansu Ga Venezuela October 16, 2025 Sojojin Pakistan Sun Tarwatsa Tankokin Yaki 6 Na Afghanistan A Rikicin kan Iyaka October 15, 2025 Tawagar Super Eagles Ta Nijeriya Ta Lallasa Benin Da ci 4-0 A Uyo October 15, 2025 Matakin Kasashen Yamma Na Maidowa Da Iran Takunkumi Ya Sabawa Doka. October 15, 2025 Kasar Indunusiya Ta Sanar Da Goyon Bayanta Ga Alummar Falasdinu October 15, 2025 Isra’ila Za Ta Sake Kai Hare-hare Idan Ta Karbi Dukkan Mutanenta Da Hamas Ta Kama. October 15, 2025 Trump Ya Fadawa Hamas Su Mika Makamansu Ko Kuma A Kwace Su Da Karfi October 15, 2025 Iran Ta Samarda Sabbin Hanyoyi Na Fuskantar Barazanar Makiya October 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci