Aminiya:
2025-08-09@11:23:19 GMT

Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja

Published: 9th, August 2025 GMT

Shugaban Hukumar Yaki da Cin Masu Karya Tattalin Arziki ta Ƙasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya bayyana cewa yawancin gidajen da aka yi watsi da su a Babban birnin Tarayya, Abuja, an gina su ne da kuɗin da ma’aikatan gwamnati suka sace.

Olukoyede ya yi wannan bayani ne a ranar Laraba a wani taron tattaunawa da zauren lauyoyi na Law Corridor ta shirya, mai taken “Muhimman Matsaloli da ke Addabar Harkar Gidaje a Najeriya.

Ya shaida wa mahalarta taron cewa EFCC ta kafa wata tawaga ta musamman da za ta fara binciken irin waɗannan gine-gine.

“Za mu fara bibiyar dukkan gidajen, ba a Abuja kaɗai ba, har da sauran sassan Najeriya. Muna son sanin wa ke da su,” in ji Olukoyede.

Shugaban na EFCC bayyana cewa wasu daga cikin gidajen sun shafe fiye da shekaru goma, ba tare da an kammala su ba.

Ya ce, “Za ka yi mamaki ka ji cewa wasu daga cikin waɗannan gidaje sun shafe shekaru 10 zuwa 20 a ba a kula su. Ana fara gina su, sai a bar su haka. Babu wanda ya san dalili.”

Ya ce binciken EFCC ya nuna cewa yawancin gidajen an gina su ne da kuɗin da ma’aikatan gwamnati suka sace. Bayan sun bar aiki kuma ƙofar satar kuɗaɗen ta toshe, sai su bar aikin ginin. Daga nan sai masu gina su su fara neman masu zuba jari don kammala aikin.

Olukoyede ya ce hukumar ta fara neman ƙwace gidaje kusan 15 a baya-bayan nan, kuma tana samun ƙarin bayanai.

A jawabinsa ga mahalarta taron, shugaban na EFCC ya ce,  “Wasu daga cikin ku da ke zaune a wannan dakin, wataƙila wasu daga cikin waɗannan gidaje naku ne.

“Amma nan ba da daɗewa ba, za mu haɗu da ku a kotu, domin ba za mu iya bunkasa wannan fanni ba idan aka ci gaba da irin wannan hali. Na san wasu daga cikinku kuna da halatattum hanyoyin samun kuɗi.”

Olukoyede ya gargaɗi lauyoyi da masu gine-gine da kada su ’yan barandan masu aikata laifin wanke kuɗi.

A nasa bangaren, Shugaban Ƙungiyar Lauyoyi ta Najeriya (NBA), Afam Osigwe, ya buƙaci a samar da tsarin tantance mallakar kadarori a ƙasa baki ɗaya.

Ya kuma yi gargaɗin cewa soke  mallakar ƙasa ba tare da cikakken bayani ba — musamman saboda rashin biyan harajin ƙasa — na iya hana masu zuba jari daga ƙasashen waje shigowa.

“Dole ne mu tabbatar da gaskiya da daidaito a harkar mallakar fili idan muna son jawo masu zuba jari daga ƙasashen waje,” in ji Osigwe.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kuɗaɗen sata wasu daga cikin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gargaɗi maƙarrabansa cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin da aka ɗora masa, ya yi murabus.

Wannan gargaɗi na zuwa ne bayan murabus ɗin Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi, ya yi biyo bayan belin wani da ake zargin dilan miyagun ƙwayoyi, Sulaiman Danwawu.

Manoma sun koka kan rabon takin gwamnati a Sakkwato Hatsarin Mota: Yadda hanyar Lambata ke laƙume rayuka a Neja

Wannan lamari ya tayar da ƙura, wanda hakan ya sa Gwamna Abba, ya ɗauki mataki.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, gwamnan ya bayyana rashin jin daɗinsa kan lamarin.

Hakan ta sa ya jaddada buƙatar dukkanin mambobin majalisar da sauran manyan jami’an gwamnati su kasance masu gaskiya da riƙon amana.

“Ba za mu lamunci kowace irin ɗabi’a ta ƙashin kai da za ta ci gaba da lalata ƙimar gwamnatinmu ba,” in ji Gwamnan.

“Dukkanin ma’aikata dole su kasance masu lura da kuma ɗaukar nauyin ayyukansu. Ba ofishinku kawai kuke wakilta ba, kuna wakiltar gwamnatinmu.”

Gwamnan ya ƙara da cewa duk wanda ba zai iya sauke nauyin amanar da aka ɗora masa ba, ya yi murabus da kansa maimakon aikata wani abu da zai ɓata sunan gwamnati.

Ya kuma nanata cewa yaƙi da miyagun ƙwayoyi da sauran munanan ɗabi’u a cikin al’umma yana daga cikin ginshiƙin mulkinsa.

Ya ce duk wanda aka samu yana da hannu kai-tsaye ko a kaikaice wajen taimaka wa masu aikata irin waɗannan laifuka, zai fuskanci hukunci.

“Mun hau mulki da kyakkyawan manufa ta daidaita al’amura, gaskiya da ci gaba a Jihar Kano. Wannan buri ba zai taɓa taɓewa ba,” in ji shi.

Wannan mataki da gwamnan ya ɗauka na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ke ƙara barazana ga matasa da zaman lafiyar al’umma a jihar.

Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da adalci, gaskiya da kyakkyawan shugabanci ga al’ummar Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fashewar gurneti ya kashe yara uku a Borno 
  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
  • Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC
  • Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci
  • Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina
  • Hatsarin Mota: Yadda hanyar Lambata ke laƙume rayuka a Neja