Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu
Published: 8th, August 2025 GMT
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce kasarsa ta kammala shirin amfani da sojoji wajen mamaye ilahirin Zirin Gaza na Falasdinawa domin ya koma karkashin ikonta.
A cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar da safiyar Juma’a, Netanyahu ya tabbatar da shirin inda ya ce, “Sojojin Isra’ila za su shirya karbe iko da Zirin Gaza baki daya sannan a samar wa fararen hula agaji a wajen yankunan da ake gwabza yaki.
Kazalika, wasu majiyoyi biyu daga gwamnatin Isra’ila sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa duk hukuncin da majalisar tsaron kasar ta yanke zai bukaci amincewar majalisar zartarwar kasar, wacce ita kuma ba za ta zauna ba sai ranar Lahadi.
Mamayar Gaza dai wani muhimmin mataki ne a yakin da kasar take yi a yankin na Falasdinawa wanda zai iya tilasta wa dubban mutane barin gidajensu.
Bugu da kari, dubban Falasdinawa na fama da matsananciyar yunwa saboda yadda Isra’ila ta toshe dukkan kofofin shigar da kayan tallafi zuwa yankin.
Sannan a ranar Alhamis, Netanyahu ya sanar da cewa ko da kasarsa ta kammala mamaye yankin, ba ita za ta shugabance shi ba, wasu za ta ba su rika gudanar da shi bisa kulawarta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Falasdinawa Isra ila Netanyahu
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Gaza
Shugaban Kasar Iran ya jaddada cewa; Dole ne kasashen musulmi su hana ci gaba da aikata laifuka a Gaza
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, yayin wata tattaunawa ta wayar tarho da fira ministan Malaysia Anwar Ibrahim, ya jaddada bukatar kasashen musulmi su dauki matakin hana ci gaba da bala’in jin kai a Gaza ta hanyar diflomasiyya da kuma matsin lamba na siyasa.
A safiyar yau Laraba ne shugaba Pezeshkian ya tattauna da fira ministan Malaysia Anwar Ibrahim ta wayar tarho, inda ya jaddada cewa: “Aikin ta’addancin da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta aiwatar a Gaza ba abin da za a amince da shi ba ne ga kowane mai ‘yanci,” yana mai bayyana fatansa na ganin “kasashen Musulmi za su yi aiki tare da hadin kai, ta hanyar diplomasiyya mai inganci, don hana ci gaba da wadannan laifuka.”
Pezeshkian ya kuma kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kasance mai kare hakkin al’ummar Falastinu da ake zalunta, inda ta yi kira ga sauran kasashen musulmi da su kara daukar matakai masu tsauri da tasiri wajen nuna goyon baya ga Gaza.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Taya Ali Larijani Murnar Nada Shi Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran August 6, 2025 An Fara Gudanar Da Juyayin Cikan Shekaru 80 Da Harin Amurka Da Makamin Nukiliya Kan Hiroshima Na Kasar Japan August 6, 2025 Dakarun Kai Daukin Gaggawa Na Sudan Sun Kashe Fararen Hula 14 Tare Da Jikkata Wasu Na Daban August 6, 2025 IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran August 6, 2025 ‘Yansanda A Iran Suna Amfani Da Kayakin Tsaro Na Zamani A Lokacin 40 August 6, 2025 Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin August 6, 2025 Iran Ta Ce Babu Wani Da Zai Kusanci Cibiyoyin Tashe Makamashin Uranim Na Kasar August 6, 2025 Iran: Yakin Kwanaki 12 Ya Bayyana Inganci Da Karfin Yakin Yanar Gizo Na Kasar August 6, 2025 Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa August 6, 2025 Sheikh Qassem: Tsaron Isra’ila zai rushe cikin sa’a 1 idan ta shelanta yaki a kan Lebanon August 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci