Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu
Published: 8th, August 2025 GMT
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce kasarsa ta kammala shirin amfani da sojoji wajen mamaye ilahirin Zirin Gaza na Falasdinawa domin ya koma karkashin ikonta.
A cikin wata sanarwa da ofishinsa ya fitar da safiyar Juma’a, Netanyahu ya tabbatar da shirin inda ya ce, “Sojojin Isra’ila za su shirya karbe iko da Zirin Gaza baki daya sannan a samar wa fararen hula agaji a wajen yankunan da ake gwabza yaki.
Kazalika, wasu majiyoyi biyu daga gwamnatin Isra’ila sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa duk hukuncin da majalisar tsaron kasar ta yanke zai bukaci amincewar majalisar zartarwar kasar, wacce ita kuma ba za ta zauna ba sai ranar Lahadi.
Mamayar Gaza dai wani muhimmin mataki ne a yakin da kasar take yi a yankin na Falasdinawa wanda zai iya tilasta wa dubban mutane barin gidajensu.
Bugu da kari, dubban Falasdinawa na fama da matsananciyar yunwa saboda yadda Isra’ila ta toshe dukkan kofofin shigar da kayan tallafi zuwa yankin.
Sannan a ranar Alhamis, Netanyahu ya sanar da cewa ko da kasarsa ta kammala mamaye yankin, ba ita za ta shugabance shi ba, wasu za ta ba su rika gudanar da shi bisa kulawarta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Falasdinawa Isra ila Netanyahu
এছাড়াও পড়ুন:
He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana
Mataimakin firaministan kasar Sin He Lifeng ya gana da tawagar ‘yan majalisar wakilan Amurka karkashin jagorancin Adam Smith a yinin yau Litinin 22 ga wata a birnin Beijing.
He Lifeng ya ce, a ranar 19 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaba Donald Trump sun yi wata tattaunawa ta wayar tarho, kuma sun cimma muhimmiyar matsaya, tare da samar da jagoranci bisa manyan tsare-tsare don tabbatar da daidaiton dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka a mataki na gaba. Kasashen Sin da Amurka na da sararin yin hadin gwiwa da kuma samun moriyar juna.
Ana sa ran Amurka za ta sa kaimi wajen yin magana da kasar Sin bisa ka’idojin mutunta juna, da zaman lafiya da samun nasara ga ko wane bangare, da kara amincewa da juna, da kawar da shakku, da sa kaimi ga habaka dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka. Ana fatan mambobin majalisar wakilan Amurka za su himmatu wajen samar da hanyoyin zantawa, da inganta tattaunawa da mu’amala, da kuma taka rawar gani wajen ci gaban kasashen biyu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp