Leadership News Hausa:
2025-08-11@14:20:30 GMT

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

Published: 11th, August 2025 GMT

‘Yan Ta’addar ISWAP Sun Kashe Shugaban Mafarauta A Borno

Wasu da ake zargin ‘yan ta’addar ISWAP ne sun kashe shugaban kungiyar mafarauta a kauyen Garjang da ke karamar hukumar Damboa a jihar Borno. Majiyoyi, a cewar Zagazola Makama, kwararre a fannin yaki da ‘yan tada kayar baya, ya ce lamarin ya faru ne da misalin karfe 5 na safiyar Lahadi. Kungiyoyin Kwadago Sun Tsunduma Yajin Aiki A Taraba Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19 Wanda aka kashe mai suna Habu Dala mai shekaru 53, ‘yan ta’addan ne suka dauke shi daga gidansa, inda suka bi da shi ta hanyar Mulharam zuwa kauyukan Forfot da ke karamar hukumar Damboa.

An tattaro jama’ar kauye ne domin neman Dala amma daga baya suka tarar da gawarsa dauke da raunukan harbin bindiga, inda Dakarun Operation Hadin Kai, ‘na Civilian Joint Task Force (CJTF)’, da kuma ‘yan kungiyar mafarauta suka ziyarci wurin. An kai gawar mafaraucin da ya rasu zuwa babban asibitin Damboa, inda aka tabbatar da mutuwarsa, daga bisani kuma aka mika shi ga iyalansa domin yi masa jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF), ta kai hare-hare ta sama a yankin Rann, wani gari da ke Jihar Borno, wanda ake zargin ya zama mafakar ’yan ta’adda.

Wannan aiki na cikin shirin Operation Haɗin Kai, kuma ya yi sanadin hallaka ’yan ta’adda da dama.

’Yan damfara 2 sun shiga hannun ’yan sanda a Yobe PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Wasu mazauna yankin sun bayyana cewa ’yan ta’addan sun fara guduws bayan yunƙurinsu na kai hari sansanin sojoji ya ci tura.

Da suka hangi jiragen yaƙi na sojojin sama, sai suka fara tserewa daga maɓoyarsu, amma an kashe da yawa daga cikinsu ta hanyar ɓarin wuta.

Wani mazaunin Rann ya ce da farko sun yi zaton cewa ’yan ta’addan ne za su kai musu hari saboda ƙarar da suka ji kamar ta bindiga.

Daga baya ne suka fahimci cewa sojoji ne ke gudanar da aiki.

Mai magana da yawun Rundunar Sojin Sama, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya tabbatar da harin a cikin wata sanarwa.

Ya ce sun samu bayanan sirri da suka tabbatar da inda ’yan ta’addan suke, kuma bayan sojojin ƙasa sun gano su suna guduwa, sai aka aike jiragen yaƙi da suka kai musu farmaki.

Harin ya daƙile barazanar ’yan ta’addan, kuma ya dawo da zaman lafiya a yankin.

Ejodame, ya ƙara da cewa wannan aiki ya nuna irin sadaukarwar da Rundunar Sojin Sama ke yi wajen kare dakarunta da kuma daƙile duk wata barazanar ’yan ta’adda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Ta Kashe ‘Yan jaridar Al Jazeera Biyar A Gaza
  • Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Fashewar gurneti ya kashe yara uku a Borno 
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina
  • Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta, Sun Kashe Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sojoji sun yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta a Borno