An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
Published: 9th, August 2025 GMT
Wani rikici da ya ɓarke ya yi sanadin mutuwar wani manomi mai suna Irmiya Yohanna, mai shekara 40, tare da hallaka shanu da tumaki 39, a ƙauyen Kaduna da ke Ƙaramar Hukumar Bogoro, a Jihar Bauchi.
Haka kuma ’yan sanda sun ceto shanu 249 da aka yi ƙoƙarin kashewa.
Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya bayyana cewa, a ranar 7 ga watan Agusta 2025, Irmiya ya tafi gonarsa amma bai dawo gida ba.
Bayan yin bincike, aka gano gawarsa a kwance a gonarsa.
Bayan samun rahoto daga Sarkin ƙauyen, Emmanuel Bulus, ’yan sanda ƙarƙashin jagorancin DPO SP Fitoka Golda sun wajen domin yin bincike.
Sun ɗauki gawar zuwa Babban Asibitin Bogoro, inda likita ya tabbatar da mutuwarsa.
Bincike, ya nuna cewa wasu da ba a san ko su wane ne ba suka kashe shi.
Daga baya, wasu fusatattu a yankin suka kai wa dabbobin Fulani hari a kusa da ƙauyen, inda suka kashe shanu 20 da tumaki 19, sannan suka jikkata wasu.
Sai dai rundunar ta kama wani mutum mai suna Ahmadu Mairiga da ake zargi da hannu a kisan.
Rahoton ’yan sanda ya ce rikicin ya fara ne lokacin da Irmiya ya tarar da shanu suna cin amfanin gonarsa.
Ya nemi makiyayan su fitar da su, sai faɗa ta kaure a tsakaninsu wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyara yankin, inda ya gana da shugabannin Fulani, sarakuna da shugabannin al’umma.
Ya gargaɗi mazauna yankin da su guji tashin hankali tare da tabbatar da cewa za su ɗauki matakan tsaro don kawo zaman lafiya.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
Ana zargin wasu ‘yan sanda daga Sashen Binciken ‘yan sanda na Kasa sun kutsa inda ake tsare dan gwagwarmaya Omoyele Sowore a Abuja, inda suka fita da shi da karfin tuwo zuwa wani wuri da har yanzu ba a sani ba. Haka kuma kamar yadda Sowore ya sanar a shafinsa na sada zumunta na Facebook, ya yi zargin cewa an karya hannunsa yayin da jam’an suka finciko shi da karfin tsiya daga inda yake tsare wajen qarfe 6:00 na safiyar yau Alhamis a kokarinsu na kai shi kotu ba tare da sanar da lauyansa ba.. A jiya Laraba ne dai Sowore ya amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ‘Yan sanda na kasa ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ‘yan sanda suka yi a makon jiya Ana kuma son karin bayani kan zargin da Sowore ya yi na cewa, Babban Sufeton na Kasa ya kara wa jami’an ‘yan sandar da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba. Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton na kasa Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa. Tuni dai Kungiyar kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar yin Allah wadai da kamun da hukumar ‘yan sandan ta Najeriya ta yi wa Sowore wanda ta ce ya sba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki. Haka kuma Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba. Shi ma dan gwagwarmaya Bello Galadanci da aka fi sani da Dan Bello, ya yi tir da kamun da aka yi wa Sawore tare da kiran a sake shin an take kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Facebook.