Aminiya:
2025-09-24@11:18:34 GMT

An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi

Published: 9th, August 2025 GMT

Wani rikici da ya ɓarke ya yi sanadin mutuwar wani manomi mai suna Irmiya Yohanna, mai shekara 40, tare da hallaka shanu da tumaki 39, a ƙauyen Kaduna da ke Ƙaramar Hukumar Bogoro, a Jihar Bauchi.

Haka kuma  ’yan sanda sun ceto shanu 249 da aka yi ƙoƙarin kashewa.

Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya bayyana cewa, a ranar 7 ga watan Agusta 2025, Irmiya ya tafi gonarsa amma bai dawo gida ba.

Bayan yin bincike, aka gano gawarsa a kwance a gonarsa.

Bayan samun rahoto daga Sarkin ƙauyen, Emmanuel Bulus, ’yan sanda ƙarƙashin jagorancin DPO SP Fitoka Golda sun wajen domin yin bincike.

Sun ɗauki gawar zuwa Babban Asibitin Bogoro, inda likita ya tabbatar da mutuwarsa.

Bincike, ya nuna cewa wasu da ba a san ko su wane ne ba suka kashe shi.

Daga baya, wasu fusatattu a yankin suka kai wa dabbobin Fulani hari a kusa da ƙauyen, inda suka kashe shanu 20 da tumaki 19, sannan suka jikkata wasu.

Sai dai rundunar ta kama wani mutum mai suna Ahmadu Mairiga da ake zargi da hannu a kisan.

Rahoton ’yan sanda ya ce rikicin ya fara ne lokacin da Irmiya ya tarar da shanu suna cin amfanin gonarsa.

Ya nemi makiyayan su fitar da su, sai faɗa ta kaure a tsakaninsu wanda hakan ya kai ga mutuwarsa.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani-Omolori Aliyu, ya kai ziyara yankin, inda ya gana da shugabannin Fulani, sarakuna da shugabannin al’umma.

Ya gargaɗi mazauna yankin da su guji tashin hankali tare da tabbatar da cewa za su ɗauki matakan tsaro don kawo zaman lafiya.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Kisan jami’an tsaro na cigaba da zama ruwan dare a Najeriya, lamarin da ya daɗe yana tayar da hankali, amma a ‘yan kwanakin nan abin ya ƙara muni.

 

Misali, kwanan nan a an kashe wasu jami’an ‘yan sanda a kananan hukumomin Katsina-Ala da Ukum a jihar Benue, inda ‘yan bindiga suka kai hari tare da kashe ‘yan sanda uku inda suka kuma sace wasu bakwai.

NAJERIYA A YAU: Yadda Wata Bakuwar Cuta Take Cin Naman Jikin Mutanen Malabu DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan abin da dokokin kasa suka ce kan kisan jami’an ‘yan sanda.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa
  • Mahara sun kashe ɗan sanda, sun ɗauke bindigarsa a Taraba
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Doka Ya Ce Kan Kisan Jami’an ‘Yan Sanda
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina
  • Mahara sun kashe ’yan sanda a shingen bincike a Kogi
  • Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja