Mazauna kauyuka akalla 30 daga Dan-Isa da Kagara dake karamar hukumar Kaura-Namoda a jihar Zamfara, sun mamaye gidan gwamnati dake Gusau babban birnin jihar domin nuna takaicinsu kan yadda rashin tsaro a yankin na su “yaki ci yaki cinyewa” a ranar Alhamis. Masu zanga-zangar da suka hada da mata da kananan yara suna dauke da alluna dauke da rubuce-rubuce kamar: “Muna bukatar zaman lafiya a kauyukan Kaura-Namoda,” “Gwamna Dauda Lawal da Matawalle ku kawo mana dauki”, “Ana kashe mu kowace rana,” da dai sauransu.

Tsoffin Kansilolin APC Sun Yi Zanga-zangar Nesanta Kansu Da Maganganun Abdullahi Abbas  Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Jihohin Makwabta, Ya Kara Ta’azzarar Rashin Tsaro A Neja – Bago Da yake jawabi a gidan gwamnati, jagoran masu zanga-zangar, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya ce sun gudanar da zanga-zangar ne don nuna takaicinsu kan yadda ’yan bindiga ke addabar kauyukansu tare da kashe mutanensu a koda yaushe. “Dukkanmu mun fito ne daga kauyuka kusan 30 don nuna rashin amincewa da rashin tsaro saboda yawancin mutanenmu ko dai an kashe su ko kuma ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su. “Suna bukatar a biya su kudin fansa da ya kai miliyoyin Naira, alhalin ba mu da komai, babu abin da za mu bayar a matsayin kudin fansa, domin duk mun sayar da kadarorinmu da gonakanmu domin biyan kudin fansar ‘ya’yanmu da ‘yan uwanmu da aka yi garkuwa da su a baya,” in ji Kamilu. Masu zanga-zangar sun yi kira ga Ministan Tsaro, Bello Matawalle, da gwamnatin tarayya karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu da su kawo musu dauki, suna masu cewa “Yanzu Zamfara na hannun Ubangiji mai rahama, Madaukakin Sarki”.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 

Sanarwar ta ƙara da cewa, Gwamna Lawal ya jaddada cewa tsarin dimokuraɗiyyar Kanada, ƙarfafan tattalin arziƙi, hakar ma’adinai ta hanyar da ta dace, da kuma harkokin kasuwanci masu zaman kansu masu kirkire-kirkire sun sanya ta zama abokiyar haɗin guiwar da ta ta dace ga Afrika.

 

Ya ce, “Idan Afrika za ta cika burinta gaba ɗaya, dole ne mu gane cewa ci gaba ba wai kawai batun manufofin ƙasa bane; yana kuma buƙatar aikace-aikacen matakan jihohi da ƙananan hukumomi.

 

“Yayin da Gwamnatocin Tarayya ke ba da jagorar manufofi, a matakin Jihohi, larduna, da Ƙananan Hukumomi ake fassara alƙawuran kasuwanci, zuba jari da ci gaba zuwa ainihin gaskiya.

 

“Matakan jihohi sune inda manoma ke noma abincin da ke ciyar da ƙasashe, inda aikin haƙar ma’adinai ke yin nasara ko faɗuwa, inda matasa ke neman dama, da inda masu zuba jari ke bukatar tsari mai bayyana, kwanciyar hankali, da dawowa mai adalci. Wannan shi ya sa kasancewata a nan a matsayin Gwamnan Zamfara ba da gangan bane, illa da nufin ƙarfafawa. Yana nuna cewa tashin hankali na Afrika zai samo asali ne daga jihohi da larduna kamar yadda zai fito daga manyan birane.”

 

Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa na canza tsarin mulki a Zamfara da yanayin saka jari don jawo hankalin abokan hulɗa masu gaskiya waɗanda ke da darajar gaskiya, rikon amana, da ci gaba mai ɗorewa.

 

“Noma shi ne ginshiƙin tattalin arziƙinmu. Fiye da kashi 70 na ƙasar mu tana da filin noma, Zamfara na iya zama amfanin gona ga Nijeriya da ma nahiyar Afrika. Muna neman haɗin kai a fannonin injina, ban ruwa, kula da amfanin gona bayan girbi, ajiya, da sarrafa kayan gona. Kwarewar Kanada, haɗe da jajircewar manomanmu, na iya samar da sabon tsarin tsaron abinci ga Afrika.

 

“Baya ga noma, Zamfara na da ma’adinai masu daraja kamar zinariya, lithium, manganese, da granite waɗanda suke da muhimmanci ga sauyin makamashi. Muna ƙoƙarin koyon darasi daga kurakurai na baya, domin tabbatar da cewa arzikin albarkatu ya fassaru zuwa ci gaba, ba wai fitarwa kawai ba. Muna ƙarfafa dokoki, inganta hakar ma’adinai na gaskiya, da tabbatar da amfanin al’umma.”

 

“Ina kira ga abokanmu na Kanada da su duba bayan manyan biranen Afrika zuwa yankuna, gonaki, makarantun, masana’antu, da al’ummomi, inda ainihin haɗin kai zai bunƙasa. Ku ƙarfafa shugabannin Afrika, ciki har da ni, wajen yin garambawul, ƙarfafa mulki, tsayawa kan gaskiya, da gina muhalli mai kyau ga haɗin kai.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • ‘Yan Gwagwarmaya  Sun Kashe Sojojin Mamaya Biyu A Wani Kwanton Bauna A Arewacin Gaza
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
  • Taron Canada: Haɗin Gwiwa Afirka Ke Buƙata Ba Agaji Ba – Gwamnan Zamfara 
  • Italiya: An yi gagarimar zanga-zangar tir da kisan kiyashi da ake yi a Gaza
  • Yawan Kudin Da Aka Kashe Na Zamantakewa A Watan Agusta A Kasar Sin Ya Kai RMB Triliyan 3.97
  • Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • Karin ƙananan hukumomi 2 sun yi sulhu da ’yan bindiga a Katsina