Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga
Published: 8th, August 2025 GMT
Daruruwan mazauna kauyen Jimrawa da ke karamar hukumar Kauran Namoda a jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a Gusau babban birnin jihar kan matsalar tsaron da ta addabe su.
Hakan na zuwa ne mako biyu bayan mazauna Gusau din su ma sun yi irin wannan zanga-zangar kan cewa ’yan bindiga sun kashe sama da mutum 100 a kauyukan jihar.
Kauyukan da aka kashe mutanen sun hada da Mada, Ruwan Bore, Fegin Baza, Lilo da kuma Bangi.
NAJERIYA A YAU: Shekara nawa shugabanni ke bukata don cika alkawuran zabe? Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a KanoKauran Namoda da sauran kananan hukumomin jihar dai sun jima suna fama da hare-haren ’yan ta’adda, lamarin da ya yi sanadin kisan mutane da dama da kuma lalata kauyuka masu yawa.
Mazauna yankunan dai sun ce rashin kyawun hanyoyin jihar na taimaka wa matsalar tsaron saboda jami’an tsaro na shan bakar wahala wajen kai musu dauki.
Masu zanga-zangar dai sun yi wa gidan gwamnatin jihar da ke Gusau kawanya suna neman a kai wa kauyen nasu agajin gaggawa.
Kauyen na Jimrawa dai na cikin gundumomi guda shida da Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta tsara gudanar da zaben cike gurbi ranar 16 ga watan 16 mai zuwa.
Da take jawabi a yayin zanga-zangar, daya daga cikin matan mai suna Maimuna Adamu, ta ce wasu daga cikin mazajensu yanzu haka suna hannun ’yan bindiga, dalilin da ya sa suka fito kwansu da kwarkwata don nuna bacin ransu.
“Mun zabi Dauda Lawal a matsayin Gwamna, amma tun da ya hau mulki a 2023 ya gaza cika mana alkawarin da ya dauka na inganta tsaro,” in ji ta.
Shi ma wani daga masu zanga-zangar mai suna Auwalu Umar, ya ce, “Sun kasha mahaifina da mahaifiyata da ’yan uwana maza da mata. Yanzu ni kadai nake rayuwa ba ni da mataimaki ko mashawarci.”
Shi ma wani dattijo da ya ki bayyana sunansa ya ce, “Ba za mu koma gid aba har sai mun samu tabbacin tsaro. ’Yan siyasa kawai kuri’armu suka damu da it aba rayuwarmu ba.”
Aminiya ta rawaito cewa ko a ranar Talata maharan sun sace sama da mutum 150 a wasu jerin hare-hare da suka kai kan kauyukan jihar daban-daban cikin kwana hudu kacal.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zamfara zanga zangar
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan gida ɗaya sun kitsa garkuwar ƙarya domin karɓar N5m a wurin mahaifinsu
Rundunar ’yan sandan Nijeriya reshen Abuja ta sanar da cafke wasu mata ’yan gida ɗaya da ake zargi da kitsa garkuwar ƙarya da zummar karɓar kuɗin fansa na naira miliyan biyar a wurin mahaifinsu.
Kakakin rundunar, SP Josephine Adeh, ce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar.
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 17 a Borno da Adamawa Buni ya shirya bikin karrama daliban da suka lashe gasar duniyaTa bayyana cewa sun samu tushen faruwar lamarin ne bayan da wani Mista Innocent, ya kai rahoton ɓacewar ’yarsa mai shekaru 16 a ranar 18 ga Yuli, 2025.
Mista Innocent ya shaida wa ’yan sandan cewa ’yar tasa ba ta dawo gida ba tun bayan da ta fita domin zana jarabawa a makarantar sakandare ta gwamnati da ke Karu.
Mahaifin ya bayyana cewa bayan wani lokaci ne wasu suka kira shi da waya suna neman kuɗin fansa kafin su saki ’yar tasa.
“Nan da nan DPO ɗin ofishin Jikwoyi ya ƙaddamar da bincike, inda aka bibiyi lambar wayar da aka kira da ita har aka gano cewa waɗanda suka kira suna zaune a wani gida a Jikwoyi Phase II,” in ji SP Adeh.
A cewarta, lokacin da aka isa gidan, an gano matashiyar da ake zargin an yi garkuwa da ita tare da wata mata a matsayin baƙuwa a gidan wani mai suna Mayowa Adedeji, suna cin abinci har da hira cikin natsuwa, babu wata alamar damuwa tattare da ita.
“Ƙarin bincike ya nuna cewa yayarta ce da saurayinta yayar suka shirya makircin, tare da haɗin gwiwar matashiyar da kanta,” in ji Adeh.
An gano cewa yayar matashiyar ta kista makircin da wani saurayinta, inda suka tsara yadda za su ɗauke ‘yar uwarta su ɓoye ta a gidan abokin saurayin, yayin da yayar za ta ci gaba da zama a gidan mahaifinsu domin nuna kamar ba ta da masaniya kan abin da ke faruwa.
“Ita kuwa matashiyar da aka ce an yi garkuwa da ita, ta amince da wannan shiri, kuma ta yarda za ta zauna a gidan yayin da mahaifinta ke cikin tashin hankali,” in ji sanarwar.
SP Adeh ta ce duka mutane huɗun da ake zargi suna hannun ‘yan sanda, inda nan gaba kaɗan a gurfanar da su a kotu da zarar an kammala cikakken bincike.