Masar ta yi gargadin cewa a shirye take ta dauki duk wani mataki na kare muradunta
Published: 12th, August 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Masar Badr Abdelatty ya yi gargadin cewa a shirye take ta dauki duk wani mataki na kare muradunta na iyakokin teku.
Da yake magana a wani taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Alkahira tare da ministan harkokin wajen kasar Ivory Coast, Léon Kacou Adom, wanda aka gudanar a wani bangare na shawarwarin siyasa karo na uku tsakanin Masar da Cote d’Ivoire, Abdelatty ya ce tattaunawar ta yi tsokaci kan kalubalen ci gaban kasashen Sahel da yammacin Afirka.
Ya kuma kara da cewa, an tattauna hadin gwiwa kan yaki da ta’addanci, inda ya yaba wa Cote d’Ivoire bisa kokarin da take yi a wannan fanni.
Abdelatty ya jaddada cewa, “Masar na mai da hankali matuka kan samar da tsaro da kwanciyar hankali a yankin Sahel da Afirka ta Yamma,” yana mai bayyana tasirin rashin zaman lafiya a wadannan yankuna a kan kasashe makwabta da kuma tsaron kasa na Masar.
A cewar wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Masar ta fitar, ministocin biyu sun kuma yi nazari kan sabbin abubuwan da suka faru a yankin Gabas ta Tsakiya, da yankin kahon Afirka, da kuma tekun Red Sea, tare da lalubo hanyoyin inganta zaman lafiya da tsaro da kwanciyar hankali a nahiyar Afirka.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa, bangarorin biyu sun amince su ci gaba da yin hadin gwiwa da tuntubar juna a matakai na kasashen biyu, da yin musayar ra’ayi a mataki na yankin da kuma na kasa da kasa.
A nasa bangaren, ministan harkokin wajen kasar Ivory Coast ya yaba da muhimmiyar rawar da Masar ke takawa wajen tallafawa da gina karfin kasashen yammacin Afirka da yankin Sahel, da kuma kokarin da take yi na samar da tsagaita bude wuta a zirin Gaza da saukaka isar da kayayyakin jin kai da agaji ga al’ummar Palasdinu.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi Allah wadai da kisan kiyashin da Isra’ila ta yi wa ‘yan jarida a Gaza August 12, 2025 Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata August 12, 2025 Ministan tsaron Italiya ya caccaki gwamnatin Netanyahu kan batun Gaza August 12, 2025 Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Wannan Talata August 11, 2025 Iran: Lebanon Tana Da ‘Yancin Kare Kanta Da Makamanta August 11, 2025 Mali: An Kama Sojoji Fiye da 40 Bisa Zargin Yunkurin Juyin Mulki August 11, 2025 Iraki: Larijani Da Sudani Sun Gana A Bagdaza August 11, 2025 Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu August 11, 2025 Mahukuntan Iraki: Adadin Masu Ziyarar Arba’een Daga Kasashen Ketare Zai Iya Haura Miliyan 40 August 11, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza August 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunciউৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
Welayati: Makircin Amurka da Isra’ila na kwance damarar Hizbullah ba zai yi nasara ba
Ali Akbar Velayati mashawarcin jagoran juyin juya halin Musulunci da Jamhuriyar Musulunci ta Iran kan harkokin kasa da kasa ya tabbatar da cewa “Jamhuriyar Musulunci tana adawa da shirin kwance damara na kungiyar Hizbullah” yana mai jaddada cewa Iran a ko da yaushe tana goyon bayan al’ummar kasar Labanon da kuma gwagwarmayarsu.
Da yake magana da kamfanin dillancin labarai na Tasnim na Iran a ranar Asabar, Velayati ya ce bijiro da batun kwance damarar Hizbullah ba sabon abu ba ne a Lebanon.
“Kamar yadda wannan yunƙurin ya gaza a baya, wannan karon ma ba za iyi nasara ba, kuma ‘yan gwagwarmaya zasu ci gaba da yin tsayin daka a kan manufofinsu da kuma dakile wannan makirci,” in ji shi.
Ya yi ishara da matakan siyasa da wasu bangarori na Labanon suke dauka da nufin kwance damarar Hizbullah, yana mai bayyana su a matsayin wadanda suka tasirantu da matsin lamba daga Amurka da Isra’ila.
Velayati ya ce Washington da “Isra’ila” sun yi imanin za su iya maimaita wani yanayi irin na kasar Syria a Lebanon, inda suka yi amfani da Jaulani domin aiwatar da wanan manufa, amma wannan mafarkin ba zai zama gaskiya ba, kuma Lebanon kamar kullum, za ta ci gaba da zama mai gwagwarmaya domin rayuwa a cikin martaba da karama.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu August 10, 2025 Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar August 10, 2025 Pezeshkiyan Ya Yabawa Yan Jarida A Ayyukansu A Yakin Kwanaki 12 August 9, 2025 Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa August 9, 2025 Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan August 9, 2025 Falasdinawa 11 Ne Suka Rasa Rayukansu Saboda Yunwa A Gaza August 9, 2025 Shugaban Kwango, Tshisekedi Ya Shigar Yan Tawaye A Gwamnatinsa August 9, 2025 Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shirin Share Falasdinawa Daga Kan Doron Kasa August 9, 2025 Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen August 9, 2025 Guterres: Dole Ne Gwamnatin ‘Yan Sahayoniyya Ta Gaggauta Janye Shirinta Kan Gaza August 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci