Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta cafke wasu mutane shida da ake zargin ‘yan fashi da makami da masu garkuwa da mutane ne a karamar hukumar Doma da ke jihar.

 

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar SP Ramhan Nansel ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a lafiya, ya ce jami’an sun kuma kama wani makiyayi dauke da makamai a karamar hukumar Keana ta jihar.

 

Sanarwar ta ce, jami’an sashin Doma da ke aiki da sahihan bayanan sirri daga wani dan kasa mai kishin kasa, karkashin jagorancin jami’in ‘yan sandan shiyya, sun kai samame a wata maboyar ‘yan ta’adda da ke Yelwa Ediya inda aka kama wadanda ake zargin.

 

Ya ce a yayin da ake yi musu tambayoyi, wadanda ake zargin sun amsa laifin yin garkuwa da wani kansila mai ci inda suka sace wayoyin hannunsa guda biyu.

 

Sun kuma amince da cewa sun tare hanyar Doma zuwa Yelwa ne inda suka kai hari kan wani Ibrahim Haruna Yelwa Ediya tare da kwace babur dinsa kirar Bajaj wanda kudinsa ya kai ₦970,000 yayin da ake sayar da babur din da suka sace.

 

SP Ramhan Nansel ya bayyana cewa, a yayin aikin jami’an sun kwato kudi ₦100,000 – kudaden da aka siyar da babur din da aka binne a daji, tare da babur Bajaj daya.

 

A wani labarin makamancin haka, jami’an sashin Keana sun amsa kiran da suka yi na cewa makiyayan da ke kiwo a filayen gonaki a Gidan Zaki Hassan da ke karamar hukumar Kuduku a karamar hukumar Keana, yayin da makiyayan suka yi ta harbe-harbe kafin su gudu.

 

‘Yan sandan da ke aiki da jama’ar gari sun kama wani makiyayi mai shekaru 20, sannan sun kwato bindiga samfurin AK-47 guda daya dauke da harsashi guda shida.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Shattima Jauro Mohammed, ya bayar da umarnin mika duk wadanda ake tuhuma zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi tare da gurfanar da su gaban kuliya.

 

CP Mohammed ya jaddada kudirin rundunar na tabbatar da zaman lafiya ga kowa da kowa, yana mai gargadin cewa ba za a samu mafaka ga masu aikata laifuka ba.

 

Ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu bin doka da oda kuma su ci gaba da bayar da bayanai masu inganci a kan lokaci don taimakawa ayyukan ‘yan sanda.

 

Rel/Aliyu Muraki/Lafia.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa

Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar  Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.

Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.

Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.

DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja

Wannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.

A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.

Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.

Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.

A watan Yuli 2025  Gwamna Umar Namadi ya gudanar da  bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar  Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.

Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara  tsaurara matakan tsaro da kuma samar da  tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da  zubar da jini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano