Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya sanar a yau jumma’a cewa Jamus za ta dakatar da duk wani izinin fitar da kayan aikin soji da za a iya amfani da su a zirin Gaza, biyo bayan matakin Isra’ila na mamaye Gaza.

Da yake magana bayan zaman majalisar ministoci ta Isra’ila da kuma amincewarta da shirin kwace birnin Gaza tare da mamaye shi, Shugaban gwamnatin Jamus Merz ya ce Berlin na ci gaba da ba da goyon baya ga ‘yancin “Isra’ila” na kwance damarar Hamas tare da ganin an sako fursunoni, amma kuma duk da haka basu goyon bayan duk wani mataki zai kai ga kara tabarbarewar lamurra na jin kai a Gaza.

“Gwamnatin Jamus ta yi imanin cewa matakin soji mai tsauri da aka dauka a zirin Gaza da majalisar ministocin Isra’ila ta yanke shawara a kai a daren jiya ya kara dagula hanyoyin da za a iya cimma wadannan manufofin,” in ji Merz a cikin wata sanarwa.

“A cikin wannan yanayi, gwamnatin Jamus ba za ta amince da fitar da duk wani kayan aikin soja da za a iya amfani da shi a zirin Gaza ba.”

Matakin dai ya biyo bayan ci gaba da sukar da kasashen duniya suke yi wa yakin “Isra’ila” da aka kwashe kusan shekaru biyu tana yi kan al’ummar zirin Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwar dubun-dubatar Falasdinawa, yayin da kuma kusan dukkanin yankunan da suka zama kango.

Ministoci masu tsatsauran ra’ayi a cikin kawancen Netanyahu sun matsa kaimi wajen mamaye yankin na Gaza da karfin soji, duk kuwa da gargadin da jami’an soji suka yi cewa irin wannan mataki na iya jefa rayuwar sauran fursunonin da ake tsare da su a yankin cikin hadari.

Jamus, wacce ta dade tana kawance da “Isra’ila” wadda it ace ta biyu bayan Amurka wajen taimakon Isra’ila, ta fara nuna damuwa da irin halayen da gwamnatin Netanyahu take nunawa kan batun Gaza, wanda ya jawo mata bakin jinni da kyama a duniya baki daya.

Ko a cikin watan Yuni, majalisar dokokin Jamus ta amince da lasisin fitar da kayan soji domin taimaka ma Isra’ila, wanda kimarsu ta kai Euro miliyan 485 (dala miliyan 564).

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Hizbullah: Amurka na hakoron taimaka wa ajandar Isra’ila ne a kan Lebanon August 9, 2025 Ramaphosa da Putin sun tattauna rikicin Ukraine da batutuwan da suka shafi kasashensu August 8, 2025 Australia ta gargadi Isra’ila game da yunkurin mamaye Gaza August 8, 2025 Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza August 8, 2025 Iran Ta Kira taron Gaggawa Na Kungiyar Kasashen Musulmi August 8, 2025 Iraniyawa Miliyon 1.2 Ne Suka Shiga Iraki Ta Kofar Shiga Na Mehran August 8, 2025 Ansarullah Ta Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin August 8, 2025 Hizbullah Da Amal Sun Yi Tir da Shirin Kwance Damarar Hizbullah August 8, 2025 Jirgin Daukar Marasa Lafiya Ya fadi A kasar kenya Ya Kuma Kashe Akalla mutane 6 August 8, 2025 Araqchi: Hari Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran Ba Zai Taba Canza Matsayinta Ba August 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: gwamnatin Jamus

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya

Hare-haren da Isra’ila ta kai a zirin Gaza a daren jiya ya yi sanadiyar shahadar Falasdinawa da dama tare da jikkata wasu masu tarin yawa, yayin da jiragen yakin Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke ci gaba da kaddadamar da munanan hare-hare a kan a yankuna da dama na Zirin da aka yi wa kawanya, da suka hada da gidajen farar hula da tantunan da aka kafa a mafaka  ga iyalan da suka rasa matsugunansu.

A cewar wakilin Al Mayadeen, akalla Falasdinawa biyar ne suka yi shahada, wasu kuma suka jikkata bayan da jiragen saman Isra’ila suka yi ruwan bama-bamai a wani tanti da ke a yankin Tal, kudu maso yammacin Deir al-Balah a tsakiyar Gaza.

A sansanin Nuseirat na yammacin Gaza, wani jirgin sama mai saukar ungulu na Isra’ila ya kai hari kan wani gida da ke hasumiyar al-Salhi kusa da unguwar  Abu Serrar, inda ya kashe Anas Abdul Rahman al-Jammal, da matarsa, da ‘ya’yansu mata biyu. Harin ya kuma yi sanadiyyar jikkata wasu fararen hula.

An samu karin hasarar rayuka bayan harin da Isra’ila ta kai kan iyalan da suka rasa matsugunansu a sansanin ‘yan gudun hijira na al-Bureij, da ke tsakiyar zirin Gaza.

A kudancin zirin Gaza, hare-haren da jiragen yakin Isra’ila suka kai a yankin al-Mawasi dake yammacin Khan Younis, sun yi sanadin shahadar da dama daga cikin fararen hula da suka hada da wani karamin yaro mai suna Amir Mansour mai shekaru 6 tare da mahaifiyarsa.

Hakazalika jiragen yakin haramtacciyar kasar Isra’ila sun yi ruwan bama-bamai a sansanin Khan Younis da ke yammacin Gaza, inda suka kashe Ahmad Rubhi Abu Sahloul, da matarsa, da ‘ya’yansu bayan sun kai hari a gidansu da ke unguwar al-Qatatwa.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Pezeshkian Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Yaki A Gaza August 6, 2025 Araqchi Ya Taya Larijani Murnar Zama Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran August 6, 2025 Japan: An Fara Juyayin Cikar Shekaru 80 Da Harin Amurka Na Makamin Nukiliya A Hiroshima August 6, 2025 Sudan: Dakarun RSF Sun Kashe Fararen Hula 14 Tare Da Jikkata Wasu Na Daban August 6, 2025 IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran August 6, 2025 ‘Yansanda A Iran Suna Amfani Da Kayakin Tsaro Na Zamani A Lokacin 40 August 6, 2025 Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin August 6, 2025 Azizi: Iran Ba Za Ta Bar Wani Ya Kusanci Cibiyoyinta Na Tace Sanadarin Uranium Ba August 6, 2025 Iran: Yakin Kwanaki 12 Ya Bayyana Inganci Da Karfin Yakin Yanar Gizo Na Kasar August 6, 2025 Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa August 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hizbullah: Amurka na hakoron taimaka wa ajandar Isra’ila ne a kan Lebanon
  • Australia ta gargadi Isra’ila game yunkurin mamaye birnin Gaza
  • Axios: Majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shiri na mamaye birnin Gaza
  • Human Rights Watch Ta Ce: Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Rusa Makarantu Fiye Da 500 A Gaza
  • Amurka Ta Kwace Dalar Amurka $584 Na Jami’ar California A Los Angeles Saboda Gaza
  • Amurka Ta Kwace Kudaden Jami’ar Jahar California A Los Angeles Dala Miyon $584 Saboda Falasdinu
  • Jamus: Shahararrun mutane fiye da 160 da ‘yan jarida sun bukaci a daina baiwa Israila makamai
  • Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya
  • Malaman Jami’o’in Isra’ila Sun Nemi Jamus Ta Tilasta Dakatar Da Yakin Gaza