Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Published: 11th, August 2025 GMT
Kakakin ofishin jakadancin kasar Sin a kasar Birtaniya, ya soki kalaman da kasashen kungiyar G7 suka yi, dangane da ganin baiken ‘yan sandan yankin HK, bayan da a ranar 25 ga watan Yuli da ya shude, ‘yan sandan suka fitar da takardar sammacen cafke wasu mutane 19, masu yunkurin haifar da tashin-tashina a kasar Sin da suka tsere zuwa kasashen ketare.
A ranar Asabar ne ofishin jakadancin na kasar Sin a Birtaniya, ya yi tir da kalamai marasa ma’ana da kasashe membobin kungiyar G7, ciki har da Birtaniya suka furta kan batun, yana mai cewa, wasu kasashe tsiraru ciki har da Birtaniya, sun tsoma baki a batun dokar tabbatar da tsaro, wadda ‘yan sandan yankin musamman na HK ke aiwatarwa, wanda hakan katsalandan ne cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da ma dokokin yankin na HK. Don haka, kakakin ofishin ya ce, “Muna matukar bayyana adawa da hakan.”
Jami’in ya kara da cewa, “Muna matukar goyon bayan gwamnatin yankin musamman na HK, game da yadda take aiwatar da harkokin gwamnati bisa doka, kana muna goyon bayan ‘yan sandan yankin na HK, bisa rawar da suke takawa ta kare doka, bisa la’akari da tabbatattun dokoki.”
Ya ce, yadda hadakar wadannan kasashe suka tsoma baki cikin harkokin yankin HK, ya kara fayyace matsayarsu ta yin baki biyu, da munafurci a batutuwa masu nasaba da kare hakkin bil’adama da wanzar da doka. Kuma a cewar jami’in, ba abun da hakan zai haifar sai karfafa gwiwar gwamnatin HK, wajen jagorantar yankin bisa doka da hukunta masu laifi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a Birtaniya
এছাড়াও পড়ুন:
HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin
Wata cibiyar bincike mai suna “Frensic Architecture’ ta bada sanarwan cewa, HKI tana fakewa da tsagaita budewa juna wuta a Gaza a matsayin dama ta sake shata kan iyakoki a zirin gaza.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ta nakalto cibiyar tana cewa a halin yanzu HKI ta maida ‘koren layin da Trump ya shata a shwarar tsagaita wuta da ya gabata na tsaida yaki a Gaza a matsayin sabon taswirar Gaza.
Labarin ya kara da cewa an Trump ya gabatar gabatar da wannan shawarar ce don sake tsuge fadin gaza, wanda kuma a halin yanzi sojojin hki suna hana Falasdinawa a gaza zuwa kusa da layin da suka shata, kuma duk wanda ya matso kusa da shi suka harbeshi.
Labarin ya kara da cewa tun ranar da aka tsagaiya wuta a ranar 10 ga watan Octoban shekara ta 2025 HKI ta mamaye kashe 54% na zirin Gaza inda ta kara rage fadin yankin wanda mutane fiye da miliyon biyu suke rayuwa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojoji Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar Guinea Bissau November 26, 2025 Larijani Iran Tana Maraba Da Tattaunawa Ta Gaskiya Amma Ba Tsararren Sakamako Ba November 26, 2025 November 26, 2025 Isra’ila Tana Ci Gaba Da Rushe Gidaje A Yankin Gaza November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci