“Baya ga alaƙa da Ruwa, ƙasashen da ke Afirka ta Gabas da kuma waɗanda ke a Afrika ta Tsakiya, da suke yi musharaka da irin ƙalubalensu da kuma sauran damarmakinsu, dole ne mu zage mu amfana da tattalin arzikin da ake da shin a Tekuna, musamman ta hanyar haɗa kanmu da kuma yin haɗaka, wanda idan ba a yi hakan ba, tamkar muna kawai yaudarar kawunan mu ne,” Ɗantso ya ce.

A cewar Shugaban na Hukumar NPA, alƙaluman da ake da su, sune za su bamu damar, ci gaba da ɗaukar matakan da suka kamata, na wajen ci gaba da bai wa Tashoshin Jiragen Ruwa na Afrika, kulawar da ta dace.

Kazalika, Shugaban ya kuma jinkinawa shugaban ƙasa Bola Tinubu, kan ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, inda ya sanar da cewa, hakan ya samar wa da Hukumar ta NPA sauƙi wajen samar da inagantattun sauye-sauyen a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan ƙasar.

“Gwamnatin mai girma Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa ƙirƙiro da Ma’aikatar Kula da Tattalin Arziki na Teku, hakan ya samar wa da Hukumar mu ta NPA samun sauƙin samar da ingantattun sauye-sauye, a fannin na tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwan Ƙasar nan, inda kuma ta hanyar Ma’aikatar, a ƙara samar da ɗimbin masu zuba hannun jari a fannin tare da kuma amfana da basira ƙwararrun da ke a ƙungiyar ta PMAWCA,” Inji Shugaban.

Ɗantsoho ya ci gaba da cewa, ƙwararrun da ke kula da kafar sadarwar, suma suna ci gaba da taimaka wa wajen ƙara samar da horo domin a amfana da damarmakin da ke a Tashoshin na Jiragen Ruwan, musamman ta hanyar amfani da tsarukan PCS NSW.

Shugaban na Hukumar ta NPA ya ƙara da cewa, dole ne, a ci gaba da yin ƙoƙarin da ake gudanarwa kafaɗa da kafaɗa, ta hanyar haɗa kai da sauran ‘ya’yan ƙungiyar ta PMAWCA.

“Manufofin yarjejeniyar kasuwanci marar shinge ta Afrika wato AfCFTA, sun haɗa da kawar da haraji da kuma duk wani harajin da ke sanya wa, na gudanar da hada-hadar kasuwanci, wanda hakan zai kuma ƙara samar da sauran damarmaki a fannnin da kuma ƙara samun ɗaukaka fannin,” Inji Ɗantsoho.

Ɗantsoho ya ƙara da cewa, a taron da Dakaratocin na ƙungiyar ta PMAWCA suka gudanar, sun yi nazari kan samakon ayyukan da ƙungiyar ta gudanar shekarar 2024 tare da kuma auna shawarwarin da mahalarta taron suka bayar, a lokcin taron, inda suke tsara matakan da za su ɗauka nag aba, domin ƙungiyar, ta ƙara samun ci gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gaɓa Ruwa ƙungiyar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano

Hukumar Tsaro ta Sibil Difens a Jihar Kano, ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi a Ƙaramar Hukumar Doguwa.

Hukumar ta miƙa su ga Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA), domin ci gaba da bincike da gurfanar da su a kotu.

’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno

Kwamandan hukumar na Jihar Kano, Bala Bawa Bodinga ne, ya bayyana hakan yayin da yake magana da ’yan jarida a hedikwatar hukumar a ranar Juma’a.

Ya ce an kama mutanen ne da sanyin safiyar ranar Talata, 7 ga watan Oktoba, 2025, bayan samun sahihin bayaai.

Jami’an hukumar daga sashen Doguwa sun tare su a ƙofar Riruwai da ke Doguwa yayin da suke ɗauke da manyan jakunkuna uku cike da tabar wiwi.

Babban wanda ake zargi shi ne Yusuf Alasan, mai shekara 25, tare da abokan aikinsa biyu; Muktar Musa da Musa Sani.

Kwamandan, ya ce hukumar ta kammala binciken farko kuma ta miƙa su tare da kayan da aka kama zuwa ofishin NDLEA na Jihar Kano don yin ƙarin bincike.

Bodinga, ya ƙara da cewa NSCDC za ta ci gaba da aiki tare da sauran hukumomin tsaro domin kawar da laifuka da tabbatar da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a a faɗin jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano