Aminiya:
2025-09-24@14:15:58 GMT

NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026

Published: 7th, August 2025 GMT

Hukumar NAHCON mai kula da sha’anin aikin Hajji a Nijeriya NAHCON, ta bayyana cewa an ƙayyade naira miliyan 8.5 a matsayin kafin alƙalami na kuɗin kujerar aikin Hajjin 2026.

NAHCON ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis, bayan gudanar da taro da shugabanni da kuma sakatarorin hukumomin aikin hajji na jihohin ƙasar.

An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato ’Yan sanda sun ƙwato jariri da aka sace a asibitin Ekiti

Mai magana da yawun NAHCON, Fatima Sanda Usara, ta ce an ƙayyade ƙafin alƙalamin kuɗin kujerar domin fara shirye-shiryen ibadar ta wannan shekarar ta Musulunci.

Hajiya Fatima ta ambato shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, yana cewa an ƙayyade miliyan 8.5 ɗin ne a matsayin kafin alƙalami na aikin hajjin baɗi, kafin a kammala tattaunawa don sanin haƙikanin kuɗin.

Ya ce Saudiyya ta sake bai wa Nijeriya gurbin kujeru 95,000, kamar yadda ta samu a bara.

Farfesa Usman ya kuma yaba wa shugaba Bola Tinubu bisa irin goyon baya da yake bai wa hukumar da kuma alhazan Nijeriya.

A cewarsa, ƙoƙarin da gwamnatin tarayyar ta yi ne ma ya sa kamfanonin jirage suka amince suka karɓi biyan kuɗi da naira daga wajen alhazai a bara maimakon dala, domin saukaka musu.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Birtaniya Zata Amince Da Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Sakkwato Ta Dakatar da Karɓar Kuɗin Makaranta
  • Mawaki Davido ya ba matarsa kyautar motar miliyan 240
  • UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya
  • Babban Bankin Nijeriya Ya Rage Kuɗin Ruwan Da Bankuna Ke Caja
  • Kasar Sin Ta Mallaki Kusan Tashoshin Fasahar 5G Miliyan 4.65
  • CBN ya rage kuɗin ruwa zuwa kashi 27 cikin 100
  • Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha
  • Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80
  • Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
  • Birtaniya Zata Amince Da Falasɗin A Matsayin Ƙasa