Aminiya:
2025-10-13@15:50:04 GMT

Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA

Published: 11th, August 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen ruwan sama mai karfi da zai iya haifar da ambaliya a jihohi 15 na Arewacin Najeriya da wasu wurare 68, a cikin kwanaki biyar masu zuwa.

Wannan gargadi ya fito ne daga Cibiyar Lura da Gargadin Ambaliya ta Kasa, karkashin Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, inda aka bukaci hukumomi da al’umma su dauki matakan gaggawa don kare rayuka da dukiyoyi.

Cibiyar ta bayyana jerin jihohi da wuraren da ambaliyar za ta iya shafa sun hada da:

Adamawa: Jimeta, Mubi, Mayo-Belwa, Wuro-Bokki, Yola, Farkumo Bauchi: Jama’a Nasarawa: Keffi Kaduna: Jaji, Kafanchan, Zaria, Birnin-Gwari Katsina: Katsina, Bindawa, Kaita Kebbi: Kamba, Kangiwa, Kalgo, Ribah, Sakaba, Saminaka, Gwandu, Jega, Bunza, Birnin Kebbi, Bagudo, Argungu Kano: Bebeji, Gwarzo, Karaye, Sumaila, Tundun-wada Niger: Rijau, Ibi, Chanchaga, Magama, Mashegu, Minna, Mokwa, New-Bussa, Sarkin Pawa, Wushishi Taraba: Duchi Jigawa: Miga, Ringim, Hadejia, Dutse Yobe: Potiskum, Dapchi, Gasma, Gashua, Jakusko Zamfara: Kaura Namoda, Maradun, Shinkafi, Bungudu, Gusau Sokoto: Sokoto, Gagawa, Gada, Goronyo, Isa, Wamakko, Silame, Makira Borno: Bama Kwara: Jebba

Hukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.

NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA

Hukumar Kula da Halin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana cewa kawo yanzu mutane 140,228 a jihohi 21 ne ambaliya ta riga ta shafa a shekarar 2025.

Alkaluman da NEMA ta fitar sun nuna ceaw ambaliyar ta riga ta raba mutane 49,205 da muhallansu, ta lalata gidaje 10,663, da kuma gonaki 9,454 a al’ummomi daban-daban.

Jihohin da ibtila’in ya fi shafa sun hada da:

Imo (28,030), Ribas (22,345), Adamwa (12,613), Abia (11,907), Delta 8,810, Borno (8,164), Kaduna (7,334), Bayelsa (5,868) da Legas (5,793).
Sauran jihohin sun hada da Akwa Ibom (5,409), Niger (3,786), Ondo (3,735), Edo (3,234), Kogi (2,825), Sokoto (1,916), Kwara (2,663), Kano (1,446), Jigawa (1,428), Gombe (972), Anambra (925), da Babban Birnin Tarayya (1,025).

Mutanen sun kunshi maza 28,505 da mata 43,531, yara 62,393, tsofaffi 5,799 da nakassu 1,887.

Da haka hukumar ta bukaci jama’a da hukumomi da su dauki matakan gaggawa don rage illar ambaliya da kare lafiyar jama’a.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ambaliya matakan gaggawa Yanayi

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade

Al’ummomin dake garin Warwade da kewaye a karamar hukumar Dutse ta jihar Jigawa sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta yashe madatsar ruwa ta Warwade wanda ta kasance daya daga cikin hanyar samun aikin dogaro da kai ga Mazauna yankin.

Wakilinmu Usman Mohammed Zaria ya ziyarci al’ummomin da ke zaune a kusa da mmadatsr ruwan wanda aka gina ta sama da shekaru hamsin da suka gabata.

Madatsar ruwan ta Warwade ta kasance hanyar samun sana’o’in dogaro da kai ga mazauna yankin, wadanda suke kamun kifi da noman rani domin samun na yau da kullum.

Malam Umar Sani, wanda masunci ne a Warwade, yace da abin da yake samu daga kamun kifi yake kula da iyalan shi da kuma sauran bukatun yau da kullum.

Yace ana samun ribar kimanin naira dubu goma zuwa ashirin a kowace rana daga siyar da kifin ga matafiya da kuma baki masu kai ziyara garin.

A don haka, Umar yayi kira ga gwamnatin jihar Jigawa da ta yi yashen madatsar ruwan saboda a samu karin kifaye da kuma ruwa da za a iya amfani da shi domin noman rani.

Shi ma a yayin tattaunawa da Dagacin Warwade, Malam Musa Ado, ya ce madatsar ruwan tana samar da ayyukan yi ga matasan yankin, tare da hana tafiya zuwa cirani a sauran yankunan kasar nan da sunan yin sana’o’i.

Ya ce matasan yankin suna gudanar da sana’ar kamun kifi da kuma nomar rani da ta damina.

Sai dai kuma, Malam Musa ya koka kan rashin samar da injinan noman rani da kuma Malaman gona kamar yadda ake yi a gwamnatocin baya.

Kazalika, yace a ‘yan kwanakin baya gwamnatin jihar Jigawa ta kai ziyara kauyen inda ta sanar da cewar Bankin duniya zai samar da wasu kudade ta hannun gwamnatin tarayya wanda za’a baiwa gwamnatocin jihohi domin yashewa tare da gina burtuloli da hanyoyin noman rani.

Bisa haka ne dagacin yayi kira ga gwamnatin jihar da ta fara yin garambawul a madatsar ruwan domin a baiwa mazauna yankunan damar amfani da shi.

A shekarun baya dai, gwamnatin jihar Jigawan ta samar da irin kifaye guda dubu Dari uku domin inganta samar da kifi a yankin.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  
  • Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya