Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara

A cewar Goɓspend, an kashe maƙudan kuɗaɗe a ƙarƙashin mulkin Shugaba Tinubu a tsakanin Afrilu da Agusta 2024 wajen kula da jiragen saman shugaban ƙasa.

Farkon kashe kuɗaɗen a ranar 14 ga Yulin 2023, lokacin da aka biya naira miliyan 846.03 a matsayin kuɗaɗen tafiye-tafiyen shugaban ƙasa na wucin gadi. Kwanaki biyu daga bisani, an sake kashe naira miliyan 674.82. A wannan watan kaɗai, jirgin ya laƙume sama da naira biliyan 1.5.

A watan Agusta, kashe kuɗaɗen sun ƙaru. An kashe naira biliyan 2 a ranar 16 ga Agusta, kuma an rubuta ƙarin kuɗaɗe na naira miliyan 387.6 da naira miliyan 713.22 a wannan watan. A cikin zangon ƙarshe na shekara ta 2023, an kashe naira biliyan 1.26 a watan Nuwamba.

Shekarar 2024 ma ta fara ne da ƙarin kashe kuɗaɗe masu yawa. A watan Maris kaɗai, an kashe kuɗaɗe har sau biyu na naira biliyan 1.27 kowanne a ranar 7 da 9 na wannan watan. Wannan ya biyo bayan nai-ra biliyan 5.08 a ranar 23 ga Afrilu, wanda shi ne mafi girma a cikin kashe kuɗaɗe a watanni 18 da aka gudanar da binciken.

A ranar 8 ga Mayu da 11 ga Mayu, an kashe naira biliyan 2.43 da naira biliyan 1.27 a jere, tare da wani ƙarin naira biliyan 1.27 da aka aike a ranar 25 ga Mayu. A ranar 5 ga Agusta, gwamnatin ta baya naira biliyan 1.25 da naira biliyan 2.21, sannan a ranar 6 ga Agusta, naira miliyan 902.9 da naira biliyan 1.24 aka kashe. Jimlar dukkanin abin da aka kashe a watan Agusta ya kai sama da naira biliyan 5.6.

Biyan kuɗin ya ci gaba har zuwa ƙarshen kwata na hudu na 2024, duk da haka a cikin ƙarancin adadi. Waɗanda sunka haɗa da naira miliyan 160.4, a ranar 8 ga Agusta, naira miliyan 35, a ranar 11 ga Sa-tumba, naira milian 133, a ranar 29 ga Satumba, da jerin biyan kuɗaɗe masu ƙaranci a Disamba, ciki har da na naira miliyan 290 da naira miliyan 102.95 da naira miliyan 25.25 da naira miliyan 8.7.

Jirgin saman shugaban ƙasa, wanda rundunar sojin saman Nijeriya ke kula da shi, ana amfani da shi ne wajen yin sufuri na sama na shugaban ƙasa da mataimakin shugaban ƙasa da manyan jami’an gwamna-ti. Duk da cewa yana da matuƙar muhimmanci, amma kuɗaɗen da ake kashewa wajen kulawa da jirgin ya kasance batun da ake tattaunawa da sukan lamarin, musamman ma a cikin yanayin matsalolin kuɗi da Nijeriya kef ama da shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da naira miliyan da naira biliyan naira biliyan 1 kashe kuɗaɗe kashe naira

এছাড়াও পড়ুন:

Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu

Ƙasar Birtaniya a wannan Lahadin za ta amince a hukumance da kafa ƙasar Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta.

Birtaniya wadda ta daɗe tana goyon bayan Isra’ila za ta juya mata baya, sakamakon hare-haren da Isra’ilar take kai wa Zirin Gaza, wanda ya samo asali bayan da ƙungiyar Hamas ta kai wani mummunan hari a ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Jami’ar European-American ta musanta bai wa Rarara digirin girmamawa An sanya tukwicin N10m domin kama makasan limamin coci a Enugu

Tun a watan Yulin wannan shekarar Firaministan Birtaniya, Keir Starmer ya ce zai goyi kafa ƙasar Falasɗinu yana mai gindaya wa Isra’ilar sharaɗin yanke wannan shawarar.

Starmer ya ce zai amince da ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ilar ba ta ɗauki wani ƙwaƙƙwaran mataki na cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da Hamas ba kafin babban taron Majalisar Dinkin Duniya na watan Satumba.

Kafafen yada labarai sun ruwaito cewa, Starmer zai yi jawabi ga al’umma kan matsayarsa, gabanin babban taron zauren majalisar Dinkin Duniya, inda ƙasashe 10 ciki har da Faransa za su amince da kafa ƙasar ta Falasɗinu.

Sai dai Amurka da Isra’ila sun soki matakin, suna bayyana shi a matsayin saka wa Hamas duk da harin da ta kai na ranar 7 ga watan Oktoban 2023.

Su ma ƙasashen Portugal da Canada da Australia sun ce za su amince da ƙasar Falasɗinun a cikin wannan mako.

Daga gobe Litinin ce sama da shugabannin ƙasashe 140 ne za su hallara a birnin New York domin taron shekara-shekara na Majalisar Ɗinkin Duniya.

Matsalar jinƙai da ta addabi yankin Falasɗinu za ta kasance a kan gaba a tattaunawar da za ta gudana a taron na bana.

Shugaba guda da ba zai halarci taron a zahiri ba shi ne shugaban Falasɗinawa, Mahmud Abbas, wanda Amurka ta hana biza tare da waɗansu jami’ansa.

A karo na musamman, babban zauren ya kaɗa ƙuri’a a ranar Juma’a domin bai wa Abbas damar gabatar da jawabi ta hanyar bidiyo, yayin da jakadan Falasɗinu zai wakilce shi a cikin ɗakin taron.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun ci ribar Naira biliyan 601 a watanni shidan farkon 2025 – Bankin GT
  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • UNGA: Shettima Ya Tallata Damar Zuba Jari Na Dala Biliyan 200 A Fannin Makamashi A Nijeriya
  • Majalisa ta ɗage ranar dawowarta zuwa 7 ga watan Oktoba
  • Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau
  • Yawan Kudin Da Aka Kashe Na Zamantakewa A Watan Agusta A Kasar Sin Ya Kai RMB Triliyan 3.97
  • Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York
  • Birtaniya za ta amince da ƙasar Falasɗinu