Gwamnatin Jihar Jigawa  ta raba katin duba sakamakon jarabawa ga ɗalibai sama da dubu shida da ɗari biyar da suka kammala makarantun sakandaren Larabci da suka yi nasarar rubuta jarabawar NBAIS ta shekarar 2025 a jihar.

 

Shugaban Hukumar Ilimin Addinin Musulunci ta Jihar, Dakta Mubarak Abdulwahab Hassan ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

 

A cewarsa, dukkan ɗaliban aji na ƙarshe na makarantun sakandaren Larabci na gwamnati da suka amfana da wannan tallafi sun kammala rubuta jarabawar NBAIS makon da ya gabata, kuma suna jiran sakamakon.

 

Ya ce wannan tallafi na daga cikin ɗawainiyar da gwamnatin Gwamna Umar Namadi ke yi wajen taimaka wa ɗaliban aji na ƙarshe na sakandaren Larabci domin duba sakamakon nasu cikin lokaci, musamman ga waɗanda ke da niyyar ci gaba da karatu.

 

Dakta Mubarak Abdulwahab ya ƙara da cewa tun bayan zuwan wannan gwamnati, hukumar ilimin addinin Musulunci ta samu kulawa sosai daga gwamnati, musamman a fannin gyaran makarantu, katange makarantun, ƙirƙirar ƙarin makarantun sakandaren Larabci, da inganta matsayin ilimin addinin Musulunci a makarantun sakandare da sauran fannoni.

 

Saboda haka, Shugaban Hukumar ya roƙi malamai da shugabannin makarantun sakandaren Larabci a jihar su mayar da martani kan wannan kyauta ta hanyar ƙara himma wajen gudanar da ayyukansu domin cimma nasarorin da ake buri.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jarabawa Jigawa makarantun sakandaren Larabci

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Cutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.

 

A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu kuwa gani suke yi zaki da maiko ne ke kawo ta.

Wannan shine abun da da yawa daga cikin mutane suka sani kan wannan cuta, sai dai masana kiwon lafiya na da nasu fahimtar daban kan wannan cuta.

NAJERIYA A YAU: Rashin aikin yi da hanyoyin magance su a Najeriya DAGA LARABA: Yadda ‘Yanbindiga Ke Amfani Da Hakar Zinare Wajen Mallakar Makamai

Shirin Najeriya  A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan cutar basir da hanyoyin magance ta.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyukan Cigaban Jihar Jigawa
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa
  • NAJERIYA A YAU: Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Cutar Basir
  • An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu