Gwamnatin Jihar Jigawa  ta raba katin duba sakamakon jarabawa ga ɗalibai sama da dubu shida da ɗari biyar da suka kammala makarantun sakandaren Larabci da suka yi nasarar rubuta jarabawar NBAIS ta shekarar 2025 a jihar.

 

Shugaban Hukumar Ilimin Addinin Musulunci ta Jihar, Dakta Mubarak Abdulwahab Hassan ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

 

A cewarsa, dukkan ɗaliban aji na ƙarshe na makarantun sakandaren Larabci na gwamnati da suka amfana da wannan tallafi sun kammala rubuta jarabawar NBAIS makon da ya gabata, kuma suna jiran sakamakon.

 

Ya ce wannan tallafi na daga cikin ɗawainiyar da gwamnatin Gwamna Umar Namadi ke yi wajen taimaka wa ɗaliban aji na ƙarshe na sakandaren Larabci domin duba sakamakon nasu cikin lokaci, musamman ga waɗanda ke da niyyar ci gaba da karatu.

 

Dakta Mubarak Abdulwahab ya ƙara da cewa tun bayan zuwan wannan gwamnati, hukumar ilimin addinin Musulunci ta samu kulawa sosai daga gwamnati, musamman a fannin gyaran makarantu, katange makarantun, ƙirƙirar ƙarin makarantun sakandaren Larabci, da inganta matsayin ilimin addinin Musulunci a makarantun sakandare da sauran fannoni.

 

Saboda haka, Shugaban Hukumar ya roƙi malamai da shugabannin makarantun sakandaren Larabci a jihar su mayar da martani kan wannan kyauta ta hanyar ƙara himma wajen gudanar da ayyukansu domin cimma nasarorin da ake buri.

 

Usman Mohammed Zaria

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jarabawa Jigawa makarantun sakandaren Larabci

এছাড়াও পড়ুন:

Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12

Ma’aikatar kudi ta kasar Sin, ta ce tallafin gwamnati na samar da ilimi kyauta ga daukacin daliban dake ajin karshe a makarantun share fagen shiga firamare a kasar zai amfani mutane kusan miliyan 12.

 

Yayin wata ganawa da manema labarai a yau Alhamis, mataimakin ministan ma’aikatar kudin kasar ta Sin Guo Tingting, ya ce karkashin wannan tallafi, iyalai da yaransu za su ci gajiyarsa za su samu ragin kashe kudaden makaranta da yawansu ya kai kusan yuan biliyan 20, kwatankwacin dalar Amurka biliyan 2.8. (Saminu Alhassan)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
  • Yadda ma’aikatan gwamnati ke gina gidaje da kuɗin sata a Abuja
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Mayar Da Dalibai 184 Da Suka Zo Hutu Daga Cyprus
  • Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
  • Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
  • Gwamnatin Kwara Ta Horar Da Manoma Sama Da 500 Tare Da Basu Tallafi
  • Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
  • Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano