Aminiya:
2025-08-08@16:42:04 GMT

PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Published: 8th, August 2025 GMT

Jam’iyyar PDP ta ce za ta ɗauki mataki kan wasu mambobinta da ke aikata abubuwan da ke kawo wa jam’iyyar koma baya.

Shugabancin jam’iyyar ya fi damuwa da mambobin da ke bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu don sake tsayawa takara a zaɓen 2027.

Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu Tinubu zai kashe tiriliyan 1.

5 wajen gina layin dogo na zamani a birnin Kano

Mai magana da yawun jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba, ya ce wasu fitattun mambobin jam’iyyar na yin magana a kafafen watsa labarai tare da ƙalubalantar jam’iyyar.

A cewarsa wasu ma suna bayyana shirinsu na taimaka wa jam’iyyar APC ta samu nasara a zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa.

Ya ce hakan babbar barazana ce ga jam’iyyar PDP.

A cewar kundin tsarin mulkin PDP, babu wani mamba da zai haɗa kai da wata jam’iyya ko ƙungiya don rage ƙarfan jam’iyyar ko gwamnatin PDP.

Ologunagba, ya ƙara da cewa irin waɗannan ayyukan suna haifar da rabuwar kai, rikici da ficewar mambobi daga jam’iyyar, wanda ka iya rage ƙarfinta a zaɓe mai zuwa.

Don haka, Kwamitin Gudanarwa na PDP (NWC) ya yi gargaɗi mai ƙarfi ga waɗanda ke aikata irin waɗannan abubuwa.

Ya kuma buƙaci da su daina, ko kuma su fuskanci hukunci mai tsauri bisa tsarin jam’iyyar.

Jam’iyyar ta kuma buƙaci dukkanin mambobinta su kasance masu biyayya tare da ci gaba da shiri don tunkarar babban taronta na ƙasa da zai gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, daga 15 zuwa 16 ga Nuwamban 2025.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi Goyon Baya Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

A cewar mahaifin marigayen, Dankama, ya bayyana cewa ba ya gida lokacin da katangar ta fado, inda ya ce ya kadu da jin labarin.

 

“Wannan lamarin ya faru da kusan mutane goma, amma mutane 6 sun riga mu gidan gaskiya. A yanzu haka, uku suna kwance a asibiti suna karbar magani,” kamar yadda ya shaida wa manema labarai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifin Ɗan Bello ya rasu
  • Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari
  • Gwamnan Kano ya gargaɗi muƙarrabansa bayan murabus ɗin Kwamishina
  • Tinubu Ya Umurci A Bada Kulawar Lafiya Kyauta Ga Tsofaffin Ma’aikata Masu Karamin Fansho
  • IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran
  • Iran tana Goyon Bayan Zaman Lafiya Tsakanun Kasashen Yankin
  • Ruftawar gini ta kashe uwa da ’ya’yanta 5 a Katsina
  • Kotu ta hana jagoran adawa Maurice Kamto takarar shugaban ƙasa a Kamaru
  • Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina