Cibiyar binciken duniyar wata, karkashin hukumar kula da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya ta kasar Sin, ta sanar da cewa, zuwa karo na 9, kasar Sin ta samar da kasar duniyar wata da jimilar nauyinta ya kai gram 125.42, ga kwararru masu nazarin kimiyya da fasaha na kasashe daban daban, ciki har da kason kasar duniyar wata da aka raba ma wasu hukumomin bincike 7 na kasashe 6.

Kana bisa gudanar da bincike kan kasar da na’urorin binciken duniyar wata na kasar Sin, wato Chang’e-5, da Chang’e-6, suka dawo da ita, masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin da na sauran kasashe, sun gabatar da sakamakon bincike fiye da 150.

An ce, tsarin da ake bi wajen neman samun kasar duniyar wata, shi ne a mika bukatar samun kasar ta wani shafin yanar gizo mai alaka da ayyukan binciken duniyar wata da sararin samaniya na kasar Sin. Daga baya wasu kwararru na kasar Sin za su tantance bukatar da aka mika, gami da yanke shawara kan ko za a ba da kasar ko a’a.

Ban da haka, bayanan da hukumar kula da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya ta kasar Sin ta samar, sun nuna yadda masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin ke karkata hankalinsu daga binciken labarin kasa na duniyar wata, zuwa na fasahar amfani da albarkatun duniyar wata, da samar da tubali don share fagen aikin gini a duniyar. A cewar wani jami’in hukumar kula da zirga-zirgar kumbuna a sararin samaniya ta Sin, an yi hakan ne don shirya fasahohin da ake bukata wajen gudanar da ayyukan kai mutane duniyar wata, da gina tashar bincike kan duniyar wata, a nan gaba. (Bello Wang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a sararin samaniya kasar duniyar wata duniyar wata da na kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

 

Haka kuma, kaso 73.2 sun yi imanin cewa manyan kasashe ba sa sauke dukkan nauyin da ya rataya a wuyansu game da harkokin kasa da kasa, sannan kaso 81.9 sun yi kira ga MDD da ta kara mayar da hankali kan muradu da bukatun kasashe masu tasowa. (FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou November 5, 2025 Daga Birnin Sin Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE  November 5, 2025 Daga Birnin Sin Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka November 5, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Ukraine: Fiye Da ‘Yan Afirka 1000 Ne Suke Taya Rasha Yaki Da Kasar Ukiraniya
  • Kotu Ta Yanke Wa Wata Budurwa Hukuncin Shekaru 4 A Kano, Duba Laifinta
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
  • An gano gawar wata mai shekara 96 a cikin masai
  • An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
  • Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho
  • Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano
  • Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya