Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Published: 11th, August 2025 GMT
Jam’iyyar ADC ta zargi hukumar EFCC na yin son zuciya tare da yin aiki a matsayin kayan aikin siyasa ga jam’iyyar mai mulki APC. Jam’iyyar ta gargaɗin cewa irin wannan mataki yana rage ingancin yaƙin da ake da cin hanci da kuma rage amincewar jama’a.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Mallam Bolaji Abdullahi, ya fitar, ADC ta bayyana cewa ayyukan EFCC na baya-bayan nan, ciki har da buɗe tsofaffin shari’o’i da kuma maida hankali kan ƴan adawa, sun nuna halayyar kamar ta “mai aiwatar da umarnin siyasa” maimakon hukuma mai aiki da gaskiya.
ADC ta jaddada cewa an kafa EFCC ne domin tabbatar da adalci ta hanyar aiwatar da doka a kan kowane ɗan Nijeriya ba tare da wariya ba, amma yanzu wannan hangen nesan da aka yi ya lalace. Ta zargi hukumar da barin shari’o’in da suka shafi abokan APC su shuɗe ba tare da kulawa ba, yayin da take tsananta bincike kan ƴan adawa, lamarin da ke ƙara tabbatar da ra’ayin cewa alaƙa da jam’iyya mai mulki ne ke tantance wanda za a bincika.
Jam’iyyar ta yi kira ga ƴan Nijeriya, da ƙungiyoyin farar hula da kafafen yaɗa labarai da su ƙi amincewa da duk wata alama ta mulkin kama-karya, ta kuma tunatar da EFCC cewa hukuma ce ta ƙasa wadda ake ɗaukar nauyinta daga harajin jama’a, ba sashi a jam’iyya mai mulki ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya
A safiyar wannan Litinin ɗin ce aka wayi gari da wani mummunan hatsarin tankoki biyu na dakon iskar gas a Zariya, inda direba ɗaya kacal ya tsira da rai, yayin da wasu da dama suka ƙone ƙurmus.
Shaidun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe tara na safe, a kusa da shatale-talen Jirgin Sama Mota da ke titin Kaduna zuwa Zariya, daura da sabuwar Kasuwar Ɗan Magaji.
An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’aniRahotanni sun nuna cewa motocin biyu sun gogi juna ne yayin da ɗaya ke ƙoƙarin wuce ɗaya, lamarin da ya haddasa kamawar wuta nan take.
An ji wata ƙara mai ƙarfi da ta tashi a lokacin haɗarin, lamarin da ya tayar da hankalin mazauna yankin.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, mutane da dama sun yi ta tserewa daga gidajensu domin guje wa abin da ka iya zuwa ya komo, yayin da kuma hayaƙi mai yawa ya mamaye hanyar da ya daƙile zirga-zirgar ababen hawa.
Jami’an tsaro da na kashe gobara sun kai ɗauki wurin domin ceto mutane, amma ƙarfin wutar ya hana su samun damar kaiwa kan motocin.
Shugaban Sashen Kula da Hatsari na Ƙasa (FRSC) reshen Zariya, Nasir Abdullahi Falgore, ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon goguwar motocin dakon gas ɗin biyu, saɓanin raɗe-raɗin cewa tsautsayin ya rutsa da wasu ƙananan motoci ƙirar Golf.
“Direban ɗaya daga cikin motocin ya tsira, kuma mun kai shi asibiti domin samun kulawa. Shi kaɗai ne zai iya ba da cikakken bayani idan ya samu sauƙi,” inji Falgore.
Shugaban Ƙungiyar Direbobi a Zariya, Malam Sa’idu Haruna, ya bayyana cewa ana yawan samun hatsari a wurin saboda yanayin kwana da titin yake da shi.
“Kusan duk wata biyu zuwa uku sai an sami hatsari a nan. Muna kira ga hukumomi su kawo ɗauki,” inji shi.
Haka kuma, shugaban bayar da agajin gaggawa na ƙaramar hukumar Sabon Gari, Abdul Malik Aminu, tare da na Zariya, Abdul’muminu Adamu, sun tabbatar da cewa ba a gama tantance adadin mutanen da suka rasu ba saboda akwai fasinjoji a motocin da ba a gano su ba tukuna.
DPO na ofishin Ɗan Magaji, CSP Auwalu A. Sani, ya ce aikinsu shi ne sanya ido don kare rayukan masu wucewa, amma bai bayar da ƙarin bayani kan hatsarin ba.