Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@15:50:02 GMT

Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila

Published: 11th, August 2025 GMT

Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta karfafa matakan tsaro a yankin Babanla biyo bayan harin da wasu da ake zargin mahara ne suka kai musu, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, SP Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce ‘yan fashi da makami da yawansu ya kai daruruwa, a kan babura, sun mamaye al’ummar Babanla a karamar hukumar Ifelodun.

 

A cewarsa wadanda ake zargin sun kai hari ne a hedikwatar ‘yan sanda inda suka kai farmaki cikin kasuwar.

 

Ya bayyana cewa maharan sun yi ta harbe-harbe kai-tsaye, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.

 

Sanarwar ta ce jami’an ‘yan sanda, jami’an Sojin Najeriya, ‘yan banga, da mafarauta cikin gaggawa sun dakile harin, tare da dawo da zaman lafiya, tare da fara farautar wadanda suka kai harin.

 

Ya yi nuni da cewa kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kwara, Adekimi Ojo, tare da rakiyar daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), sun kai ziyarar tantancewa Babanla domin tantance yanayin tsaro.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samar da wani babban tsari domin tabbatar da zaman lafiya da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da tsaro a cikin al’ummar da lamarin ya shafa.

 

Ta ce tawagar jami’an tsaron hadin gwiwa sun zagaya muhimman wurare a cikin al’umma – ciki har da kasuwa, da hedikwatar ‘yan sanda, da kewaye domin tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da kyautar motoci ƙirar Hilux guda shida da babura 30 domin taimaka wa sojoji wajen yaƙi da ’yan bindiga a faɗin jihar.

Gwamnan, ya miƙa motocin da baburan ga Kanal Hussaini Rabi’u Toro na rundunar sojoji ta takwas a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi

Ya ce wannan kyauta na cikin ƙoƙarin gwamnatinsa na tabbatar da tsaro da walwalar al’umma.

“Tsaro shi ne babban abin da gwamnatina ta mayar da hankali a kai. Ba za mu yi wasa da harkar tsaro ba.

“Za mu ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro da dukkanin abin da suke buƙata,” in ji Gwamna Idris.

Ya ƙara da cewa, an fara bai wa sojoji ne kyautar, amma sauran hukumomin tsaro su ma za su samu irin wannan tallafi nan ba da jimawa ba.

Da yake bayani a wajen taron, Kanal Hussaini Toro, ya gode wa gwamnan bisa wannan taimako, inda ya cewa hakan zai ƙara musu ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

“Sojoji sun yi matuƙar farin ciki da wannan tallafi. Zai taimaka wajen inganta aikinmu na tabbatar da tsaro a Jihar Kebbi,” in ji Kanal Toro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro
  • A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno