Leadership News Hausa:
2025-10-13@17:51:12 GMT

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

Published: 10th, August 2025 GMT

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta kama wanda ya kafa kuma yake kula da cocin ‘The Turn of Mercy’, Adefolusho Olasele, wanda aka fi sani da Abbas Ajakaiye, bisa zarginsa da hannu wajen safarar miyagun kwayoyi da dama daga Ghana zuwa Nijeriya. Fasto Olasele, wanda ya shafe watanni ba a san inda yake ba, an kama shi ne a ranar Lahadi, 3 ga watan Agusta, 2025, a cocinsa da ke Okun Ajah, yankin Lekki, a Legas.

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho Wata sanarwa da mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi, ya fitar a ranar Lahadi, ta ce, jami’an hukumar sun jira har zuwa lokacin da ya gama wa’azi na ranar Lahadi kafin su kama shi a lokacin da ya fito daga harabar cocin. A cewarsa, faston ya gudu zuwa Ghana a cikin watan Yuni don gujewa kama shi bayan da jami’an tsaro suka alakanta shi da laifin safarar miyagun kwayoyi  kulli biyu kimanin kilo 200 da aka gano a bakin tekun Okun Ajah a ranar 4 ga watan Yuni da kuma kilo 700 da aka samu a cikin motarsa ta kai sako a ranar 6 ga watan Yuli.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako

An kammala kada ƙuri’a da yammacin Lahadi a zaɓen shugaban ƙasa na Kamaru, inda shugaban ƙasa mai shekaru 92, Paul Biya — wanda shi ne tsohon shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya — yake neman wa’adi na takwas a mulki.

Biya, wanda ya shafe shekaru 43 yana mulkin ƙasar, ya fafata da ’yan takara 11, ciki har da tsoffin muƙarrabansa.

Ɗaya daga cikinsu shi ne Issa Tchiroma Bakary, tsohon ministan ma’aikata wanda ya yi murabus daga gwamnati a watan Yuni bayan fiye da shekaru 20 yana aiki tare da Biya.

Bakary, mai shekaru 79, ya zama babban abokin hamayyar Biya bayan Kotun Tsarin Mulki ta ƙi amincewa da takarar fitaccen ɗan adawa Maurice Kamto — matakin da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ciki har da Human Rights Watch suke cewa ya rage sahihancin tsarin zaɓen.

Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya Matasa da dogon mulki

Kamaru na da masu kaɗa ƙuri’a kusan miliyan takwas, yawansu matasa da ba su taɓa sanin wani shugaban ƙasa ba sai Biya, tun da ya hau mulki a 1982.

A cikin shekaru 20 da suka gabata, Biya yakan lashe zaɓe da sama da kashi 70 na ƙuri’u.

Bayan ya jefa ƙuri’arsa a kusa da fadar gwamnati a Yaounde, Biya ya ce wa manema labarai: “Ba a san komai ba tukuna. Mu jira mu ga wanda aka zaɓa.”

Wani jami’in hukumar zaɓe ta ƙasa, Jean-Alain Andzongo, ya shaida wa AFP cewa an gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da tsari a babban birnin.

Mai sharhi kan harkokin siyasa, Stephane Akoa, ya ce duk da cewa jam’iyyar mai mulki na da damar ganin ta sami nasara, wannan yaƙin neman ya kasance “mai ɗan ɗumi fiye da yadda aka saba,” yana nuna yiwuwar “samun wasu abubuwan mamaki.”

’Yan takara da yaƙin neman zaɓe

Biya bai yi fitowa sosai ba a lokacin yaƙin neman zaɓe, inda ya bayyana sau ɗaya kacal a wani babban gangami a Maroua, a yankin Arewa Mai Nisa — inda akwai masu kaɗa ƙuri’a miliyan 1.2.

Sai dai wannan yankin da aka daɗe ana ɗauka matsayin ginshikin goyon bayansa, yanzu wasu tsoffin abokansa ne ke takara da shi daga yankin.

’Yan adawa sun gudanar da gangami a sassa daban-daban na ƙasar, suna alkawarin kawo sauyi ga al’ummar Kamaru.

A yayin da Biya ya tara ’yan ɗaruruwan mutane kaɗan a gangaminsa, Bakary kuwa ya samu tarbar dubban magoya baya a yankin da ya fito, suna ɗaga tutoci masu taken “Tchiroma Mai Ceto.”

Tattalin arziki da ƙorafin jama’a

Duk da albarkatun ƙasar – musamman noma da ma’adinai – Kamaru na ci gaba da fama da talauci da rashin aikin yi.

Bisa ga rahoton Bankin Duniya (2024), kusan kashi 40% na ‘yan ƙasar na rayuwa ƙasa da layin talauci, yayin da rashin aikin yi ya kai kashi 35% a manyan birane.

Jama’a na ci gaba da koka kan tsadar rayuwa, ƙarancin ruwan sha mai tsafta, rashin ingantaccen kiwon lafiya da kuma matsalolin ilimi.

Matasa da neman sauyi

Akoa ya bayyana cewa matasan Kamaru na ƙaunar ganin sauyi, amma har yanzu ba su kai matakin yin zanga-zanga kamar yadda ake gani a wasu ƙasashe na Afirka da Asiya ba.

Ya ce: “Yawancin matasa sun nuna niyyar kaɗa ƙuri’a. Wannan alama ce mai kyau, amma ba ta kai matakin tayar da gagarumin yunƙuri irin na Madagascar ko Tunisia ba.”

Sauran bayanai da sakamakon zaɓe

Gwamnatin Kamaru ta bai wa masu lura da zaɓe kusan 55,000 — ciki har da wakilan Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) — damar sa ido kan zaɓen.

Kotun Tsarin Mulki na da wa’adin Oktoba 26 don fitar da sakamakon ƙarshe.

Sai dai wasu kafafen sada zumunta sun sanar da shirinsu na tattara sakamako da kansu — abin da gwamnati ta soki, tana zargin suna ƙoƙarin karkatar da ra’ayoyin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Sojoji Sun Kashe Kwamandan IPOB ‘Alhaji’, Da Wasu 26, Sun Kama 22
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Gwamna Uba Sani Ya Gana Da Ministan Ayyuka Domin Ganin An Kammala Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa