Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da dokoki guda biyu masu muhimmanci da nufin ƙarfafa harkar yawon buɗe ido da hanzarta gudanar da shari’a a faɗin jihar.

Shugaban majalisar, Yusuf Dahiru Liman, ne ya sanar da amincewar majalisar  yayin zaman, ta wanda aka gudanar a harabar majalisar da ke Kaduna.

 

Dokar farko mai taken “Dokar Kafa Hukumar Kula da Yawon Buɗe Ido, Gidajen Tarihi, Shata Wurare, Lambuna da Wuraren Hutu na Jihar Kaduna, 2024”, na da nufin bunƙasa harkar yawon buɗe ido da raya al’adu a  jihar.

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Yusuf Dahiru Liman

Da yake gabatar da rahoton kwamitin, Shugaban Kwamitin Haɗin Gwiwa na Harkokin Fasaha, Shari’a da Ilimi, Magaji Suleiman, ya bayyana cewa kwamitin ya gudanar da cikakken bincike kan kudirin kuma ya fahimci cewa yana da amfani wajen haɓaka yawon buɗe ido da al’adu.

Magaji Suleiman ya ce idan aka fara aiki da hukumar, za ta inganta shata wurare, lambuna da wuraren shakatawa a jihar, wanda hakan zai ja hankalin masu zuba jari daga cikin gida da waje.

A nasa jawabin, wanda ya dauki nauyin gabatar da kudirin, Mr. Henry Marah, ya bayyana cewa hukumar za ta taka rawa wajen farfaɗo da al’adun gargajiya na jihar Kaduna wacce ke da yawan kabilu daban daban.

Ya ƙara da cewa dokar za ta taimaka wajen samar da kuɗaɗen shiga ga jihar, ƙirƙiro guraben ayyukan yi ga matasa da kuma cusa tarbiyar al’adu ga matasa masu tasowa.

Barista Emmanuel Kantiyok

Har ila yau, Majalisar ta kuma amince da gyara dokar gudanar da shari’ar laifuka ta Jihar Kaduna ta shekarar 2017.

Da yake gabatar da rahoton, Shugaban Kwamitin Shari’a na Majalisar, Barista Emmanuel Kantiyok, ya bayyana cewa gyaran dokar zai taimaka wajen gudanar da shari’a a kan lokaci da kuma tabbatar da adalci ba tare da la’akari da matsayin mutum ba.

Barista Kantiyok ya ce gyaran dokar zai taimaka wajen rage cunkoso a gidajen gyaran hali da kuma ƙara wa talakawa kwarin gwiwa ga tsarin shari’a.

Majalisar ta amince da dokokin ne ta hanyar ƙuri’ar murya da ‘yan majalisar suka kada, karkashin jagorancin Shugaban Majalisar, Yusuf Dahiru Liman.

Daga ƙarshe, majalisar ta tafi hutu kuma za ta dawo zaman ta a ranar 9 ga Satumba, 2025.

 

Shamsuddeen Mannir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: jihar Kaduna Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Ɗansandan Bogi A Kano

 

A cewar kakakin rundunar ‘yansandan Kano, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa, Shitu ba jami’in ‘yansanda ba ne kuma ba konstabulari na musamman ba ne.

 

Ya kara da cewa, za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu, yayin da ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike domin sanin girman munanan ayyukansa da kuma duk wani mai hannu a ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNGA: Yau Shettima zai gabatar da jawabin Najeriya a MDD
  • Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa
  • An Kama Ɗansandan Bogi A Kano
  • Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha
  • An yi garkuwa da ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato
  • Dalilin da muke goyon bayan Tinubu kan karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Dalilin da muke goyon bayan tsare-tsaren Tinubu na karɓo bashi — Majalisar Wakilai
  • Shettima ya tafi New York don halartar taron Majalisar Ɗinkin Duniya
  • Shettima ya bar Abuja don halartar taron majalisar ɗinkin duniya a New York