Wani lokacin, yanayin shekaru da Jinsin Jini ne ke fayyace irin girma ko ƙantantar Ƙwan da Kajin za su yi.

2- Wajen Kwana:

Kajin na buƙatar a tabbatar da ana samar musu da wadataccen ruwan sha a ɗakunan kwanansu da kuma ba su kariya daga kamuwa da cutuka da rage musu wahala da cunkoso da kuma zafi, wanda hakan na iya shafar Ƙwan da za su yi kai tsaye.

3- Abinci Mai Gina Jiki:

Ciyar da su abinci mai gina jiki, wanda ke ɗauke da sinadaran ‘protein, amino acids’, waɗanda za su sanya su yi nauyi tare kuma da buƙatar a riƙa yi musu allurar ƙara musu lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwai

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Gwamnatin kasar Sin ta mika sabon kason tallafin abinci ga Zimbabwe, a wani mataki na bunkasa ikon kasar na samar da isasshen abinci ga al’ummarta, bayan matsanancin tasirin yanayin El-Nino da ya haifar da fari a shekarar bara.

Yayin bikin mika kayan abincin a jiya Alhamis, wanda aka gudanar a birnin Harare fadar mulkin Zimbabwe, mataimakiyar ministan ma’aikatar kyautata rayuwa, kwadago da walwalar al’umma a kasar Mercy Dinha, ta jinjinawa tallafin na Sin, wanda ya kunshi kimanin tan 3,000 na shinkafa da alkama, kayan da ta ce za su taimakawa ‘yan kasar mafiya fama da kunci.

A nasa bangare kuwa, jakadan Sin a Zimbabwe Zhou Ding, ya jaddada aniyar kasar Sin ta taimakawa Zimbabwe, wajen cimma nasarar wadatar da al’umma da abinci da rage talauci, yana mai cewa, tallafin bangare ne na amsa kiran Zimbabwe ga kasashen duniya, na samar mata da tallafin abinci, biyowa bayan fari da ya daidaita wasu sassan kasar.

Jakada Zhou Ding, ya ce har kullum Sin na dora muhimmancin gaske ga ayyukan samar da abinci da rage fatara. Ya kuma yi fatan kasashen biyu za su ci gaba da karfafa kawance don bunkasa samar da isasshen abinci ga al’umma. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kwara Ta Yi Gargadi Ga Manoman Ruwan Malka Na Wata Agusta
  • Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
  • Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
  • Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
  • Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
  • Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
  • Sai Ƴan Siyasa Sun Haɗa Kansu Sannan Za Su Iya Tunkarar APC A 2027 – Lukman
  • Buƙatar Katange Iyakokin Nijeriya Don Tabbatar Da Tsaro 
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana