Za A Inganta Fannin Lafiya Da Sauran Ababen More Rayuwa A Sule Tankarkar
Published: 9th, August 2025 GMT
Majalisar zartarwa ta karamar hukumar Sule Tankarkar dake Jihar Jigawa ta amince da gudanar da muhimman ayyuka a bangarorin kiwon lafiya da sauran aikace-aikacen ci gaban al’umma.
Taron majalissar bisa jagorancin shugaban Karamar Hukumar, Alhaji Tasi’u Adamu, ya kuma amince da gina makarantun Tsangaya guda 3 na zamani da za’a sanyawa sunayen wasu fitattun yan siyasa na yankin da suka rasu.
Yayi bayanin cewar, za’a gina makarantun tsangayar ne a garuruwan Danzomo da Shabaru da kuma Rukutu wadanda za’a sanyawa sunan wadanda suka rasu da suka hada da marigayi Sanata Dalha Ahmad Dan Zomo da marigayi Musa Waziri Kamus da kuma marigayi Ali Ado.
Haka kuma majalisar ta amince da gyaran masallatan Juma’a na Hannun Giwa da Dan Ladin Gumel da masallacin Tsangaya na Sule Tankarkar.
Alhaji Tasi’u yace za’a gina sabbin masallatan kamsisalawati guda 5 a garuruwan Chiromawa da Kofar Yamma da kuma Babban Sara.
Majalissar ta kuma amince da gina asibitoci matsakaita guda 3 a Dan Makama da Mabia da kuma Sarkin Gandu.
Shugaban karamar hukumar yace za’a gina magudanan ruwa da kuma samar da ruwan sha mai amfani da hasken rana a garin Lula.
Har il! yau Majalisar zartarwar ta kuma amince da sayo kayayyakin gyaran tuka tuka na naira miliyan 11 da kuma amincewa da naira miliyan 5 da dubu dari 5 domin sayen magunguna da feshin maganin sauro.
Kazalika, an amince da gyaran ofishin shugaban majalissar kansiloli da kuma ofisoshin masu bada shawara guda 7 don inganta ayyukan gwamnati a yankin.
Tasi’u, yace ayyukan na daga cikin kudirorin sa guda 5 da yayi koyi da ga cikin kudirorin Gwamna 12 domin kyautata rayuwar jama’ar yankin.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa Sule Tankarkar
এছাড়াও পড়ুন:
An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibai
Majalisar Tarayya ta amince da hukuncin cin sarƙa ga duk wani malami da aka samu da laifin cin zarafi ko lalata da ɗalibai a makarantu a faɗin ƙasar nan.
Hakan ya biyo bayan amincewar majalisar da Dokar Hana Lalata da Dalibai ta 2025 (HB.1597), bayan tsallake karatu na uku a Majalisar Dattawa da kuma Majalisar Wakilai a ranar Laraba.
Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a JosA ƙunshin bayanan da dokar, za a iya yanke wa duk wanda ya saɓa mata hukuncin ɗaurin shekara 14 ko shekara biyar mafi ƙaranci ba tare da zaɓin biyan tara ba.
Laifukan da dokar ta bayyana a matsayin cin zarafi sun haɗa da yin jima’i ko neman wata alfarma daga ɗalibai a madadin jima’i, barazana, ko tozartarwa da ɗaga hankali a wajen karatu, ko taɓawa ko rungumar jiki.
Haka kuma dokar ta haɗa da aika saƙonnin batsa, hotuna ko bidiyo, ko barkwanci ko magana mai ɗauke da cin zarafi kan jikin ɗalibi, da kuma bibiya da sa ido mai tsanani.
Sabuwar dokar, wadda ke jiran sahalewar shugaban ƙasa kafin ta fara aiki, ta bai wa waɗanda abin ya shafa damar shigar da ƙarar malamin da ya aikata laifin na cin amana.
Haka kuma dokar ta wajabta wa duk makarantu na gaba da sakandare su kafa kwamitin musamman mai zaman kansa domin kula da korafe-korafe da suka shafi cin zarafi, a bisa tsarin doka.
Dokar ta ce ba za a ɗauki yarda daga ɗalibi a matsayin hujja ta kare kai ba, sai idan ɓangarorin biyu sun yi aure bisa doka. Ta kuma bayyana cewa ba sai an tabbatar da niyyar cin zarafi ba kafin a samu hukunci.
Haka zalika, ta haramta wa makarantu gudanar da bincike na cikin gida idan an riga an kai ƙara kotu, inda ta ce har sai an gama shari’ar kafin su iya shiga tsakani.
Dokar ta kuma bai wa ɗalibai, ’yan uwa, wali ko lauya damar kai ƙara, tare da ba da damar miƙa rahoto ga rundunar ‘yan sanda ko ofishin Antoni-Janar, sannan a tura kwafin ƙarar ga kwamitin hana cin zarafi na makarantar da abin ya shafa.