Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-27@21:16:46 GMT

Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.

Published: 12th, August 2025 GMT

Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.

Yajin aikin sai baba-ta-gani da kungiyar kwadago ta Najeriya NLC reshen jihar Taraba, da kungiyar Kwadago (TUC) reshen jihar Taraba suka kaddamar a ranar Litinin da ta gabata, ya gurgunta ayyukan gwamnati a ma’aikatu da hukumomin gwamnati a jihar.

 

Matakin wanda ya fara da tsakar daren litinin, ya kasance tare da hadin gwiwar shugabannin kungiyoyin biyu bayan taron majalisar zartaswar jihar da aka gudanar a ranar Lahadi a sakatariyar kungiyar NLC ta jihar.

 

Taron ya yi nazari ne kan wa’adin da aka bayar tun da farko kan wasu kura-kuran da ake zargin an tafka a cikin ayyukan kwamitin tantance bayanan da gwamnatin jihar ta kafa.

 

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da sakataren kungiyar NLC na jihar, Adamu.W.Buba, da sakatariyar TUC ta jihar, Polina Gani suka sanya wa hannu, kungiyoyin sun umurci dukkanin rassan kungiyar da su tashi tsaye tare da kafa kwamitin aiwatar da yajin aikin domin tabbatar da an bi cikakken aikin.

 

“Dukkan ma’aikatan suna nan ta hanyar umarnin su kaurace wa wuraren aikinsu kuma su janye ayyukansu har sai wani lokaci. Za a ci gaba da yajin aikin har sai gwamnati ta biya musu bukatunsu,” in ji sanarwar “.

 

Kungiyoyin kwadago a makon da ya gabata sun zargi kwamitin da aikata ayyukan da suka yi wa ma’aikata illa tare da zargin gwamnati da yin watsi da wa’adin.

 

Shugabannin kungiyar sun bayyana cewa ba za a dakatar da yajin aikin ba har sai an gyara kura-kuran da ake zarginsu da aikatawa, inda suka bukaci masu ruwa da tsaki da su shiga Tsakani su da gwamnatin jihar.

 

Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, hukumomi daga gwamnati ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

 

COV/JAMILA ABBA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja

Wata tankar mai ta yi gobara a wani gudan mai a yankin Tungan-Bunu da ke Ƙaramar Hukumar Rijau a Jihar Neja, lamarin da ya janyo ƙonewar gidaje da kadarori da masu yawa.

Shaidu sun ce gobarar ta tashi ne a lokacin da tankar take shirin sauke mai a ranar Litinin da yamma, inda wutar ta bazu zuwa gidajen da ke kusa.

Duk da cewa babu wanda ya rasa ransa, lamarin ya haifar da firgici inda mazauna yankin suka yi ta tserewa suka bar gidajensu yayin da tankar ke ci da wuta.

Tankar mai ta yi hatsari a hanyar Lapai-Agaie Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro Mayaƙan Boko Haram sun fille kan mata 2 a Borno

A wani lamari ba daban, wata tankar mai ta kife a kan hanyar Lapai zuwa Agaie, lamarin da ya toshe hanya tare da haddasa cunkoson ababen hawa.

Shaidu sun ce tankar, wadda ke ɗauke da fetur daga Legas zuwa Gombe, ta kife ne da misalin karfe 10 na safe a ranar Litinin bayan jikinta ya rabu da kan motar, ya ƙetare hanya, abin da ya tayar da hankalin jama’a.

Wani mazaunin yankin, Malam Mahmud Abubakar, ya ce jami’an tsaro sun garzaya wajen domin tsare yankin, sannan aka tura ma’aikatan kashe gobara don kauce wa tashin wuta.

Ya ƙara da cewa lamarin ya faru ne a yankin Efu-Nda-Egbo na Ƙaramar Hukumar Lapai, inda ya haddasa cunkoson ababen hawa mai tsanani.

Kokarin tuntuɓar Darakta-Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, bai yi nasara ba, domin bai amsa kiran wayar da wakilinmu ya yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • Ko sisi ba a biya ’yan bindiga ba kafin su saki ɗaliban da suka sace – Gwamnan Kebbi
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Hizbullah: Isra’ila na kuskure idan ta na tunanin kashe-kashen kwamandodinmu zai kawo karshen kungiyar
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja