Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.
Published: 12th, August 2025 GMT
Yajin aikin sai baba-ta-gani da kungiyar kwadago ta Najeriya NLC reshen jihar Taraba, da kungiyar Kwadago (TUC) reshen jihar Taraba suka kaddamar a ranar Litinin da ta gabata, ya gurgunta ayyukan gwamnati a ma’aikatu da hukumomin gwamnati a jihar.
Matakin wanda ya fara da tsakar daren litinin, ya kasance tare da hadin gwiwar shugabannin kungiyoyin biyu bayan taron majalisar zartaswar jihar da aka gudanar a ranar Lahadi a sakatariyar kungiyar NLC ta jihar.
Taron ya yi nazari ne kan wa’adin da aka bayar tun da farko kan wasu kura-kuran da ake zargin an tafka a cikin ayyukan kwamitin tantance bayanan da gwamnatin jihar ta kafa.
A cikin wata sanarwar hadin gwiwa da sakataren kungiyar NLC na jihar, Adamu.W.Buba, da sakatariyar TUC ta jihar, Polina Gani suka sanya wa hannu, kungiyoyin sun umurci dukkanin rassan kungiyar da su tashi tsaye tare da kafa kwamitin aiwatar da yajin aikin domin tabbatar da an bi cikakken aikin.
“Dukkan ma’aikatan suna nan ta hanyar umarnin su kaurace wa wuraren aikinsu kuma su janye ayyukansu har sai wani lokaci. Za a ci gaba da yajin aikin har sai gwamnati ta biya musu bukatunsu,” in ji sanarwar “.
Kungiyoyin kwadago a makon da ya gabata sun zargi kwamitin da aikata ayyukan da suka yi wa ma’aikata illa tare da zargin gwamnati da yin watsi da wa’adin.
Shugabannin kungiyar sun bayyana cewa ba za a dakatar da yajin aikin ba har sai an gyara kura-kuran da ake zarginsu da aikatawa, inda suka bukaci masu ruwa da tsaki da su shiga Tsakani su da gwamnatin jihar.
Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, hukumomi daga gwamnati ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
COV/JAMILA ABBA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Taraba
এছাড়াও পড়ুন:
Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
A kokarin ta na ci gaba da kula da harkokin ilimi a yankin, Karamar Hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta kaddamar da aikin tantance malaman makaranta na B teach da kuma ma’aikatan lafiya na wato B health.
A jawabin sa wajen fara tantance malaman da ma’aikatan lafiyar, Shugaban karamar hukumar, Dr Muhammad Uba Builder, yace aikin tantancewar ya zama wajibi domin tabbatar da ma’aikata na gaskiya da kuma gano na bogi.
Yana mai cewar akwai rahotannin daya nuna wasu suna aiki 2 wasu kuma suna amfani da takardun bogi.
A don haka, yace duk wanda aka samu da hakan zai rasa aikin sa gami da kama shi don fuskantar hukunci.
Builder Muhammad Uba, yace an ware ranar asabar domin tantance malaman da kuma ma’aikatan lafiya domin tabbatar na gaskiya da adalci.
Yayi nuni da cewar, duk malamin da aka samu da takardun bogi, shakka babu za’a maye gurbin sa da wani.
Kazakika, Builder yaja hakalin su da su kasance masu tsoran Allah wajen gudanar da aikin su tare da ganin suna zuwa wuraren ayyukansu akan lokaci.
A jawabin sa, kansila mai gafaka na sashen ayyuka na karamar hukumar, Malam Haladu Maigari ya zayyana ayyukan raya kasa da shugaban karamar hukumar ya aiwatar karkashin jagorancin Builder Muhammad Uba.
Ya kuma baiwa malaman da ma’aikatan lafiyan shawarar fadin gaskiya na al’amurran su.
A jawaban su, jami’in shirin B Teach, Malam Nazifi Bala da kuma jami’in shirin B Health Malam mujitafa Ibrahim sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarin sa na rage zaman kashe wando ga matasan yankin karamar hukumar ta Birnin kudu.
Usman Mohammed Zaria