Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya ce ma’aikatar harkokin wajen kasar, da ofishin jakadancin kasar a Philippines, sun gabatar da korafi da babbar murya dangane da kalaman da aka jiyo jagoran Philippines na yi game da batun yankin Taiwan na Sin.

Kakakin wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, ya ce, yayin ziyarar da ya gudanar a kasar India, shugaban na Philippine ya shaidawa ‘yan jarida cewa, idan har yaki ya barke tsakanin Sin da Amurka, tabbas kasarsa za ta shiga, saboda kasancewarta a kewayen yankin, da ma ‘yan Philippines da dama dake zaune a Taiwan, wadanda ya zama wajibi a aiwatar da matakan mayar da su gida.

Jami’in Sin ya kara da cewa kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma Taiwan bangare ne na Sin da ba za a iya balle shi ba. Kazalila, batun Taiwan harka ce ta cikin gidan kasar Sin, kuma tushe na babbar moriyar kasar. Don haka warware batun yankin na Taiwan na wuyan kasar Sin ita kadai, kuma ba za ta taba hakuri da tsoma hannun wasu sassan waje ba. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

BBC Hausa ta yi nazari kan kasashen Afirka da dakarun Amurka suka shiga da sunan dakile wata matsala kamar annoba ko kuma yakar “‘yan ta’adda”.

 

Somalia (1992–1994)

Kasar Somalia ta kasance daya daga cikin wuraren da Amurka ta aika da sojojinta a wani mataki mafi girma a farkon shekarun 1990s.

A lokacin da kasar ke cikin rikicin yakin basasa da yunwa mai tsanani, Amurka ta tura sojoji don tallafawa da jigilar kayan agaji da tabbatar da zaman lafiya.

Wannan ya haifar da sanannen yakin Mogadishu da ake kira “Battle of Mogadishu” a 1993, wanda ya jawo hankalin duniya kan irin kalubalen da ke tattare da tsoma bakin soja a rikicin cikin gida.

Amurka ta kaddamar da harehare na jiragen sama a kan mayakan al-Shabab kuma ta hada kai da gwamnatin Somaliya domin dakile AlShabab.

A watan Janairu 2024 an bayar da rahoton cewa Amurka ta kashe ‘‘yan kungiyar AlShabab uku ba tare da yin wata gagarumar barna ba.

Bugu da kari, a watan Fabrairun 2025, Donald Trump ya ce ya umarci a kaddamar da hari ta sama kan wasu jagororin kungiyar IS da ke arewacin Somalia.

 

Laberiya (2014–2015)

A lokacin da cutar Ebola ta bulla a yammacin Afirka, Laberiya ta kasance cikin kasashen da cutar ta fi shafa. Amurka ta tura sojoji da kayan aiki domin taimakawa wajen dakile yaduwar cutar.

Wannan ya hada da gina cibiyoyin kula da marasa lafiya, jigilar kayan agaji, da horar da ma’aikatan lafiya.

Sai dai kuma a shekaru gabanin samun ‘yancin kai da bayan samun ‘yancin kai, Amurka ta tura dakaru zuwa kasar domin dakile yakin basasa da yan kasar suka kwashe shekaru suna fama da shi.

 

Senegal (2014–2015)

Senegal ta kasance cibiyar hadin gwiwa a lokacin barkewar cutar Ebola. Amurka ta tura sojojinta domin su bayar da tallafi na kayan aiki da kiwon lafiya don hada kai a matakan yanki.

Wannan ya taimaka wajen hana cutar ta mamaye bangaren kiwon lafiya da ya riga ya kasance da rauni a Senegal da kasashen makwabta.

 

Kenya (1998)

Bayan harin ta’addanci da aka kai wa ofishin jakadancin Amurka a Nairobi, wanda ya hallaka mutane 224, ciki har da Amurkawa 12 da kuma jikkata fiye da mutum 1000, Amurka ta tura sojojinta don bayar da agajin gaggawa, kula da marasa lafiya, da tallafawa wajen ceto rayuka.

Aikin ya fi mayar da hankali kan jin-kai da bincike.

 

Tanzaniya (1998)

Harin ta’addanci da ya shafi Kenya ya kuma shafi Dar es Salaam a Tanzaniya, kamar yadda aka yi a Nairobi, sojojin Amurka sun shiga don kula da wadanda abin ya shafa, da tallafawa wajen kare yankin daga fadawa cikin rudani, da gudanar da binciken harin kamar yadda Amurkar ta yi ikirari.

 

Libya

Sojojin Amurka sun taba kasancewa cikin Libya ta hanyoyi daban-daban, suna shiga su taya yaki da kungiyoyi irin su ISIS tare da goyon bayan kokarin kafa gwamnatin hadin kan kasa.

Haka kuma akwai lokutan da Amurka ta shiga kai tsaye: kamar harin soji da ta yi a shekarar 1986 da kuma fitowarta a cikin yakin 2011 da ya kawo karshen mulkin shugaban Muammar Ghaddafi.

Bugu da kari, tun daga watan Nuwamban 2015 har zuwa 2019, Amurka da kawayenta sun kaddamar da hare-hare ta sama da amfani da jirage marasa matuki a Libya lokacin yakin basasar da ya balle tun bayan faduwar gwamnati Muammar Ghaddafi a 2011.

 

Jamhuriyar Nijar

Kasancewar sojin Amurka a Jamhuriyar Nijar ya hada da tura dakaru na musamman da jiragen yaki marasa matuka don taimaka wa gwamnatin Nijar da Faransa wajen yaki da kungiyoyin ta’addanci a karkashin Operation Juniper Shield.

Ba a san girman adadin sojin Amurka a Nijar ba sosai har sai da aka yi harin Tongo a 2017, inda ‘yan kungiyar ISGS suka kashe sojojin Amurka hudu da na Nijar hudu, lamarin da ya jawo tambayoyi da muhawara game da dalilin da ya sa Amurka ta ajiye sojoji sama da 800 a Nijar a wancan lokaci.

A 2024 ne hedikwatar tsaro ta Pentagon ta sanar da cewa za ta kammala kwashe dakarunta daga Jamhuriyar ta Nijar ya zuwa tsakiyar Satumban shekarar bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a kasar.

Kuma a ranar 7 ga watan Yulin ne Amurkar ta kammala kwashe dukkannin sojojinta daga sansanin da ake kira da 101, inda kuma ragowar 500 da ke sansanin 201 suka fice daga kasar a ranar 5 ga watan Agustan 2024.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Mabiya Mazhabar Shi’a Sun Yi Zanga-Zanga A Kano Kan Barazanar Trump Ga Nijeriya November 8, 2025 Manyan Labarai Bisa Rakiyar Jami’an Tsaro Na Ke Ganawa Da Ƴan Bindiga – Sheikh Gumi November 8, 2025 Labarai Karramawar LEADERSHIP Gare Ni, Zaburantarwa Ce Ga Ci Gaba Da Kyawawan Manufofin Mu – Gwamna Lawal November 8, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 
  • Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi
  • Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
  • Dan Wasan Taekwando Na Kasar Iran Abulfazl Zandi Ya Zamo Shi Ne Na Daya A Duniya
  • CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
  • CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin
  • Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ita Ce Babbar Tushen Bullar Tashe-Tashen Hankula A Yankin
  • Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi
  • Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
  • Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar