Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
Published: 12th, August 2025 GMT
Dakarun Operation FANSAN Yamma (OPFY) sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda da dama a wani hari da suka kai ta sama da kasa a yankin Makakkari da ke dajin Gando a karamar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.
Wannan farmakin wanda ya gudana a ranar 10 ga watan Agustan shekarar 2025, ya biyo bayan wasu bayanan sirri da suka samu cewa dimbin ‘yan ta’addan da ke biyayya ga marigayi Halilu Buzu da Alhaji Beti sun taru a cikin dajin inda suka shirya kai harin ramuwar gayya kan al’ummomin Addabka da Nasarawan Burkullu a garin Bukkuyum.
Jami’in yada labarai na rundunar ‘Operation Fansan Yamma OPFY’ Kyaftin David Adewusi, ya ce bayanan sirri sun nuna cewa, harin da suka shirya kai harin shi ne ramuwar gayya da suka sha a baya-bayan nan a arangamar da suka yi da jami’an tsaro da wasu rundunonin tsaro.
Ya bayyana cewa, a wani samame na hadin gwiwa na kasa da ya biyo baya, dakarun da ke karkashin sashe na 2 sun kame tare da fatattakar ‘yan ta’addan da suka gudu daga inda aka kai harin ta sama.
Kyaftin Adewusi ya tabbatar wa ‘yan kasa masu bin doka da oda cewa ‘yan ta’adda da sauran masu rike da makamai ba za su samu mafaka a yankin Arewa maso Yamma da wasu sassan shiyyar Arewa ta tsakiya ba.
Ya nanata kudurin sojojin na fatattakar abokan gaba a duk inda suka taru ko kuma suka matsa sannan ya bukaci mazauna yankin da su baiwa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar ba da rahoton abubuwa, yana mai cewa bayanan da suka dace kan lokaci na da matukar muhimmanci wajen kare al’umma da kuma kawo karshen barazanar ta’addanci da ‘yan fashi.
REL/AMINU DALHATU.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sojoijn Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Runduunar ‘Yan Sandan Jihar kwara Ta Karfafa Tsaro A Banbila
Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta karfafa matakan tsaro a yankin Babanla biyo bayan harin da wasu da ake zargin mahara ne suka kai musu, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.
A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, SP Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce ‘yan fashi da makami da yawansu ya kai daruruwa, a kan babura, sun mamaye al’ummar Babanla a karamar hukumar Ifelodun.
A cewarsa wadanda ake zargin sun kai hari ne a hedikwatar ‘yan sanda inda suka kai farmaki cikin kasuwar.
Ya bayyana cewa maharan sun yi ta harbe-harbe kai-tsaye, inda suka kashe mutane 5 ciki har da dan sanda Adejumo Wasiu.
Sanarwar ta ce jami’an ‘yan sanda, jami’an Sojin Najeriya, ‘yan banga, da mafarauta cikin gaggawa sun dakile harin, tare da dawo da zaman lafiya, tare da fara farautar wadanda suka kai harin.
Ya yi nuni da cewa kwamishinan ‘yan sanda na jihar Kwara, Adekimi Ojo, tare da rakiyar daraktan hukumar tsaro ta farin kaya (DSS), sun kai ziyarar tantancewa Babanla domin tantance yanayin tsaro.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samar da wani babban tsari domin tabbatar da zaman lafiya da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da tsaro a cikin al’ummar da lamarin ya shafa.
Ta ce tawagar jami’an tsaron hadin gwiwa sun zagaya muhimman wurare a cikin al’umma – ciki har da kasuwa, da hedikwatar ‘yan sanda, da kewaye domin tabbatar da cewa an samu kwanciyar hankali.
REL/ALI MUHAMMAD RABIU