Aminiya:
2025-08-07@23:55:29 GMT

A gaggauta sakin Sowore — Atiku

Published: 8th, August 2025 GMT

Madugun adawa a Nijeriya, Atiku Abubakar ya bukaci a gaggauta sakin fitaccen ɗan gwagwarmayar, Omoyele Sowore da ke tsare a hannun ’yan sandan kasar.

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriyar wanda ya yi Allah-wadai da lamarin ya ce abin kunya ne cin zarafi da tawagar sa ido ta sufeto janar na ’yan sandan ƙasar suka yi wa Sowore.

Mahaifin Ɗan Bello ya rasu Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

“Bai dace a tsare Sowore ba, kuma hakan ya saba wa ka’ida. Dole ne a yi tur da lamarin,” in ji Atiku.

Ya ce laifin ɗan gwagwarmayar kawai shi ne don ya fito ya yi magana kan rashin shugabanci nagari da ake yi a Nijeriya.

Wasu rahotanni ma na bayyana cewa ana zargin ’yan sandan sun lakaɗa wa Sowore duka har ma an ƙarya masa hannu.

Wazirin na Adamawa ya ce wannan abin da ƴa nsanda suka aikata ba ga Sowore kaɗai ba ne, inda ya ce hakan ya nuna cewa za a far wa kowane ɗan Nijeriya da ya yi ƙoƙarin fitowa ya faɗi gaskiya.

“Don haka muna buƙatar a saki Sowore cikin gaggawa ba tare da gindaya wasu sharuɗa ba,” in ji Atiku.

A ranar Laraba ne dai aka bayar da rahoton tsare Sowore bayan da ya amsa gayyatar jami’an ’yan sanda domin amsa wasu tambayoyi.

A jiya Laraba ne dai aka bayar da rahoton tsare Sowore bayan amsa gayyatar da ofishin Babban Sufeton ’Yan sanda ya yi masa don ya amsa wasu tambayoyi da suke da alaka da zanga-zangar da tsofaffin ’yan sanda suka yi a makon jiya.

Haka kuma, an son Soworen ya bayar da bahasi kan zargin da ya yi na cewa, Babban Sufeton ya kara wa jami’an ’yan sandan da ke aiki a gidansa girma ba bisa ka’ida ba.

Sai dai ya yi watsi da zarge-zargen, inda ya bayyana su a matsayin borin kunya da hukumar ‘yan sandan take don “dauke hankalin jama’a daga abin kunyar da Babban Sufeton Kayode Egbetokun da kuma hukumar ‘yan sandan ke aikatawa.”

Tuni dai Kungiyar Kare Hakkin Bil’Adama ta Amnesty International ta fitar da sanarwar Allah wadai da kamun da aka yi wa Sowore wanda ta ce ya saba wa ‘yancinsa na fadin albakacin baki.

Haka kuma, Amnesty International ta bukaci a saki Omoleye Sowore nan take ba tare da gindaya masa wasu sharuda ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Atiku Abubakar

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifin Ɗan Bello ya rasu
  • Nazarin CGTN: Alummar Duniya Na Adawa Da Fadada Mamaya A Gaza
  • An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna
  • Ana zargin ‘yan sanda da karya hannun Sowore
  • Amurka ta Fara Janye Wasu Sojojinta Daga Wurare 3 A Kasashen Iraki Da Siriya
  • Ana zargin ‘yan sandan da karya hannun Sawore
  • Ministan tsaron Ghana da wasu sun rasu a hatsarin jirgin sama
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Uwa da Wasu Biyu Kan Ƙirkirar Garkuwa Da Kansu A Abuja
  • FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL