Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayyana cewa yara miliyan 11 da ke ƙasa da shekaru biyar a Najeriya na fama da rashin abinci mai gina jiki, lamarin da ke ƙara yiwuwar wani yanayi mai barazana ga rayuwa saboda rashin kuzari.

Shugaban Ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahma Rihood Mohammed Farah, ya bayyana haka yayin mika kayan kayan abincin na musamman da aka sayo ta hanyar haɗin gwiwar gwamnati da UNICEF a shirin Child Nutrition Match Fund, wanda aka gudanar a Cibiyar Kiwon Lafiya (PHC) ta Karamar Hukumar Takai.

Mista Rahma, wanda Daraktan Lafiya na UNICEF, Dakta Serekeberehan Seyoum Deres ya wakilta, ya ce kashi 51.9 bisa 100 na yaran Kano suna fama da mat girma saboda rashin abinci mai gina jiki, yayin da sama da kashi 10 suke fama da matsalar rashin nauyi da zai ba su kuzari.

A cewarsa, Child Nutrition Match Fund shiri ne da UNICEF ke kula da shi, tare da goyon bayan masu bayar da tallafin ƙasashen waje, inda ake bayar da kuɗi daidai-da-daidai (1:1 match funding) domin ninka jarin da gwamnatoci ke sakawa wajen samar da muhimman kayan abinci mai gina jiki.

Ya bayyana cewa Jihar Kano ta zama jagora a ƙasa wajen wannan ƙoƙari, inda ta bayar da gudummawar Naira miliyan 500 – mafi girma daga jiha guda – zuwa wannan asusu. Haka kuma shi ma asusun na UNICEF ya ƙara Naira miliyan 500, wanda ya kawo jimillar Naira biliyan 1. Wannan kuɗin aka yi amfani da shi wajen sayen kwalaye 12,948 na hadin abinci mai gina jiki da zai warkar da  yara sama da 17,000 masu fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki.

Dakta Deres ya bayyana cewa UNICEF na fassara child food poverty a matsayin rashin damar samun abinci mai gina jiki, mai yalwa, da kuma bambancin sinadaran gina jiki ga yara ‘yan ƙasa da shekaru biyar – wani lokaci mai matuƙar muhimmanci wajen haɓakar jiki da kwakwalwa.

Ya jaddada cewa UNICEF tare da hadin gwiwar masu tallafi sun samu gagarumar nasara wajen inganta abinci mai gina jiki a faɗin Najeriya, musamman a Kano.

Ya yabawa jagorancin gwamnati tare da kira ga Gwamnan Jihar Kano da ya ware ƙarin kuɗi a shekarar 2025, wanda UNICEF za ta sake bada kwatankwacinsa domin a sake sayen sinadirai da kayayyakin abincin.

Haka kuma ya bukaci a amince da manufofin bayar da hutun haihuwa na tsawon watanni shida mai ga matan da suka haihu, domin ƙarfafa shayar da jarirai nono zalla da kuma kare lafiyar jarirai da abincinsu.

Asusun na UNICEF ya sake jaddada aniyar sa ta tallafawa Jihar Kano ta hanyar haɗin gwiwar dabaru masu faɗi a fannoni daban-daban domin inganta abinci mai gina jiki da lafiyar al’umma musamman ga mata da yara.

 

Daga Khadijah Aliyu 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Kama Ɗansandan Bogi A Kano

 

A cewar kakakin rundunar ‘yansandan Kano, binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa, Shitu ba jami’in ‘yansanda ba ne kuma ba konstabulari na musamman ba ne.

 

Ya kara da cewa, za a gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu, yayin da ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike domin sanin girman munanan ayyukansa da kuma duk wani mai hannu a ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Bukaci Hada Karfi Da Karfe Wajen Gina Yankin Xinjiang Ya Zama Mafi Kyau
  • An kama ɗan sandan bogi a Kano
  • An Kama Ɗansandan Bogi A Kano
  • Iran Da Rasha Zasu Rattaba Hannun Kan Batun Gina Wasu Tashoshin Nukiliya.
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Tabbatar Da Adalci Ga Falasdinawa Wajen Maido Da Hakkinsu Na Kasa
  • Jariri ya mutu a bayan uwarsa yayin tsere wa ’yan bindiga a Neja
  • An rufe sansanin NYSC da kasuwanni saboda rashin tsaro a Kwara
  • Trump Ya Bukaci Afganistan Ta Mayarwa Amurka Sansanin Jiragen Sama Na bagram
  • ’Yan sanda sun kama mutane 5 kan zargin satar abincin yara a Borno