Al’ummar Japan na gudanar da bikin tunawa da ranar harin Nagasaki da ya faru shekaru 80 da suka gabata, wani hari da ke zama irinsa na farko kuma mafi muni da duniya ta taba gani.

Tarihi ya nuna cewa Amurka ce ta fara harba makamin Nukiliya a garin na Nagasaki kwanaki uku bayan na garin Hisroshima a wani ɓangare na dakatar da yaƙin duniya na biyu.

!

Harin na ranar 9 ga watan!!!!!!!mutane dubu 70 a take bayan mutane 140 da suka mutu kwanaki uku da suka gabata a harin na Hiroshima.

An yi ittifakin cewa wannan shine harin da ya tilastawa Japan miƙa wuya a ranar 15 ga watan Agustan wannan shekarar, matakin da ya kawo ƙarshen yaƙin.

Bayanai sun ce a yau mutane sama da 2,600 daga ƙasashe sama da 90 sun halarci taron tunawa da wannan rana a bikin da aka gudanar da filin taro na garin Nagasaki.

Firai ministan ƙasar Shigeru Ishiba ya fara buɗe taron da jawabi da misalin ƙarfe 11:02 dai-dai lokacin da makamin ya dira a garin, a wani ɓangare na girmama waɗanda suka rasa rayukansu, kafin !bisani kuma aka rika kaɗa ƙarararwa don tunawa da ruhinsu.

An saki gwamman tattabaru da ke alamta zaman lafiya bayan da shugaban ya kammala jawabi, inda ya ce wannan taro ya shiga cikin kundin tarihin ƙasar wanda za’a gajeshi ƴaƴa da kakanni.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hari

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari

Bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin tubabbun ’yan bindiga da jama’ar gari a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, mazauna yankin sun ce yanzu matsalar tsaron ta dauki sabon salo.

A watan Oktoban 2024 ne dai aka kulla yarjejeniyar sulhun tsakanin bangarorin biyu.

Yarjejeniyar na zuwa ne bayan shafe sama da shekara 10 ana fama da rikicin da ya mayar da babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari daya daga cikin mafiya hatsari a Najeriya.

Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II Ma’aikatan gwamnati na amfani da kudaden sata wajen gina rukunin gidaje – EFCC

Daga shekara ta 2015, mazauna yankin sun sha fama da hare-hare da garkuwa da su, yayin da matafiya kuma ala tilas suka koma neman rakiyar sojoji kafin su iya wuce hanyar.

Yanzu dai yankin ya fara samun saukin matsalar, yayin da mazauna yankunan suka fara komawa gidajensu manoma kuma suka ci gaba da noma gonakinsu.

To sai dai da alama yanzu a maimakon garkuwa da mutanen, rahotanni na cewa a yanzu ’yan bindigar sun fara yawo a gonaki suna kwace babura, wayoyi, kudade da ma kayan aikin gona daga hannun manoman yankin.

Mazauna kauyen Kuyello da ma wasu kauyukan sun ce yanzu suna zaman dardar.

Wasu daga cikinsu sun kyale gonakin gaba daya, wasu kuma sun ce yanzu sukan bar wayoyinsu a gida saboda tsoron za a iya yi musu fashi.

“Yanzu ’yan bindiga sun daina garkuwa da mutane, amma sun koma yi mana kwace. Yanzu suna yawo a gari hankalinsu kwance ba sa tsoron kowa,“ in ji wani mazaunin garin na Kuyello.

Hakan dai ya sake jefa tsoro a kan ingancin zaman sulhun da aka ce an yi.

Mazauna yankin dai sun yi korafin cewa babu wani yunkuri da ake yi na dakile tubabbun ’yan bindigar daga kwacen da suke yi, lamarin da ya sa suka ce suna tsoron sake komawa gidan jiya.

Bayanai dai na cewa yanzu matafiya na bin hanyar ta Kaduna zuwa Birnin Gwari, wacce babbar mahada ce tsakanin kudanci da arewacin Najeriya, ba tare da wata barazana ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh
  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara
  • An kashe matafiya biyu da yin garkuwa da uku a Kwara
  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari
  • An Fara Gudanar Da Juyayin Cikan Shekaru 80 Da Harin Amurka Da Makamin Nukiliya Kan Hiroshima Na Kasar Japan