Leadership News Hausa:
2025-11-08@18:20:31 GMT

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Published: 8th, August 2025 GMT

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

An samu mummunan iftila’i a garin Pulka na ƙaramar hukumar Gwoza a jihar Borno, inda fashewar Gurneti ya kashe yara uku a yammacin jiya Alhamis. Yaran da suka mutu sun haɗa da Fati Dahiru, Aisha Ibrahim da Fati Yakubu.

Rahoton wani masani kan yaƙi da ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana cewa, wani ɗan ƙungiyar CJTF, Buba Yaga, ya ce yaran na wasa da wani bam da ake zargin Boko Haram sun bari, kafin ya fashe da misalin ƙarfe 2:20 na rana.

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Bayan faruwar lamarin, jami’an kunce bam (EOD) na Ƴansanda, da Sojojin Operation Haɗin Kai, da CJTF, da mafarauta sun isa wurin, suka kakkaɓe wajen, kuma ba su sake samun wani abu mai haɗari ba. An garzaya da yaran asibitin gwamnati na Gwoza, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

An miƙa gawarwakin ga iyalansu don yin jana’iza bisa tsarin Musulunci, yayin da hukumomi suka shawarci jama’a su riƙa sanar da jami’an tsaro idan sun ga abubuwa masu haɗari domin kauce wa irin wannan bala’i.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia

’Yan sanda a kasar Indonesia sun ce an garzaya da daruruwan mutane zuwa asibiti bayan wani abu da ake zargin bam ne ya fashe a wani masallacin Juma’a da ke Jakarta babban birnin kasar.

Lamarin ya faru ne a lokacin sallar Juma’a a cikin wani ginin makaranta da ke Kelapa Gading, a arewaci Jakarta.

Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800

Kwamishinan ’yan sandan birnin, Asep Edi Suheri, ya ce har yanzu ana bincike don gano musabbabin fashewar.

Shaidun gani da ido sun ce sun ji fashewa biyu masu ƙarfi da misalin ƙarfe 12 na rana a agogon kasar, daidai lokacin da aka fara hudubar sallar Juma’a a masallacin.

Suheri ya ce an kai mutane 54, galibinsu ɗalibai zuwa asibiti da raunuka masu sauƙi da masu tsanani, ciki har da wadanda suka kone.

Ya ƙara da cewa mutum 20 na ci gaba da samun kulawa a asibiti, inda uku daga cikinsu ke fama da raunuka masu tsanani.

Suheri ya ce ƙungiyar ƙwararrun masu binciken bama-bamai da aka tura wurin ta gano bindigogin wasa da ƙaramar bindiga ta wasa a kusa da masallacin.

“’Yan sanda na ci gaba da binciken wurin don gano musabbabin fashewar,” in ji shi.

Kafafen yaɗa labarai na cikin gida a kasar sun nuna bidiyon da ke nuna layin ’yan sanda da ke kewaye da makarantar, inda motoci masu ɗaukar marasa lafiya ke tsaye a gefe.

Sai dai hotunan masallacin ba su nuna wata mummunar lalacewa ba sakamakon harin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NELFUND Ta Ce Dalibai Miliyan Daya Ne Suka Nemi Tallafin Kudin Karatu
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
  • An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
  • Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna
  • Unicef: Kananan Yara 47 ” Isra’ila” Ta Kashe A Yammacin Kogin Jordan
  • Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
  • Harin bam a masallacin Juma’a ya jikkata sama da mutum 50 a Indonesia
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata
  • Yara biyu sun mutu bayan faɗawa rijiya a Kano