Leadership News Hausa:
2025-08-08@16:37:42 GMT

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

Published: 8th, August 2025 GMT

Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno

An samu mummunan iftila’i a garin Pulka na ƙaramar hukumar Gwoza a jihar Borno, inda fashewar Gurneti ya kashe yara uku a yammacin jiya Alhamis. Yaran da suka mutu sun haɗa da Fati Dahiru, Aisha Ibrahim da Fati Yakubu.

Rahoton wani masani kan yaƙi da ta’addanci, Zagazola Makama, ya bayyana cewa, wani ɗan ƙungiyar CJTF, Buba Yaga, ya ce yaran na wasa da wani bam da ake zargin Boko Haram sun bari, kafin ya fashe da misalin ƙarfe 2:20 na rana.

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Manyan Shugabannin ISWAP A Borno

Bayan faruwar lamarin, jami’an kunce bam (EOD) na Ƴansanda, da Sojojin Operation Haɗin Kai, da CJTF, da mafarauta sun isa wurin, suka kakkaɓe wajen, kuma ba su sake samun wani abu mai haɗari ba. An garzaya da yaran asibitin gwamnati na Gwoza, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsu.

An miƙa gawarwakin ga iyalansu don yin jana’iza bisa tsarin Musulunci, yayin da hukumomi suka shawarci jama’a su riƙa sanar da jami’an tsaro idan sun ga abubuwa masu haɗari domin kauce wa irin wannan bala’i.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Kwamishinan ya ce tuni ya ba da umarni a fara bincike kan waɗanda ake zargin.

Ya kuma tabbatarwa da jama’a cewa duk wanda ya kawo ƙorafi za a saurare shi, ba tare da an tsananta masa ba.

A cewar rundunar, an daɗe ana samun ƙorafi cewa wasu ɓata-garin ‘yansanda suna karɓar kuɗi daga masu laifi domin su rufa musu asiri.

Amma wannan karon, hukumar za ta bi sahun ƙorafin domin ganin an yi gyara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yara Uku Sun Gamu Da Ajalinsu A Wani Tafki A Borno
  • Kasar Sin Ta Kammala Gwajin Farko Na Sauka Da Tashin Kumbon Binciken Duniyar Wata Mai Dauke Da Bil Adama
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda Fiye Da 30 A Wani Harin Jirgin Sama A Wurin Daurin Aure A Zamfara
  • Jami’ar Bayero Ta Bayyana Alhininta Bisa Kisan Gillar Wani Dalibinta
  • ‘Hayakin janareta’ ya kashe mutum 4 ’yan gida daya a Borno
  • Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
  • Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano
  • Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
  • Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano