Sudan: Sojoji na ci gaba karbe mahimman gine-gine a birnin Khartoum
Published: 23rd, March 2025 GMT
A Sudan bayan sake karbe fadar shugaban kasa da ke birnin Khartoum, sojojin kasar sun ci gaba da kai farmaki a babban birnin kasar a ranar Asabar, inda suka sake karbe iko da wasu gine-gine, ciki har da babban bankin kasa da hedkwatar hukumar leken asiri da kuma gidan adana kayan tarihi na kasar.
Ana kallon wannan a matsayin nasarorin ga Janar al-Burhan a babban birnin kasar, wanda rikicin cikin gida ya rutsa da shi na tsawon shekaru biyu.
A wannan Asabar, kakakin rundunar sojojin kasar, Janar Nabil Abdullah, ya sanar a cikin wata sanarwa cewa sojojin na ci gaba da samun nasara a birnin Khartoum, Ya kuma ce sojojin sun “kore daruruwan ‘yan bindiga.
A sa’i daya kuma, ana ci gaba da gwabza fada a yankin Darfur, wanda kusan yana karkashin ikon dakarun RSF.
A cewar masu fafutukar kare hakkin jama’a, akalla fararen hula 45 ne aka kashe a ranar Alhamis a wani harin da dakarun sa kai suka kai a garin Al-Malha da ke arewacin Darfur.
Sojojin sun yi ikirarin cewa sun yi wa garin kawanya tare da kashe makiya sama da 380.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.