Gwamnatin tarayya ta nuna damuwarta kan cewa kasar nan ta yi asarar tiriliyoyin naira sakamakon ayyukan masu hakar ma’adanai ta barauniyar hanyoyi musamman a jihohi.

Gwamnatin ta kuma cafke da gurfanar da ‘yan kasan waje su hudu wadanda suka shiga harkar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, yayin da wasu mutane 320 kuma aka cafke kan harkokin satar ma’adinai.

A cewar gwamnatin, cikin wadanda aka kama 320, kusan mutum 150 a halin yanzu suna fuskantar shari’a kuma wasu guda tara an dauresu, inda su kuma mutum hudu ‘yan kasar wajen aka dauresu a gidan yari.

Ministan bunkasa albarkatun kasa, Dele Alake, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ke ganawa da manema labarai a karshen zaman majalisar zartarwa na tarayya (FEC) wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta.

Ministan ya kuma ce, gwamnatin tarayya ta fuskanci kalubale wajen shawo kan matsalar hako zinari, musamman a arewacin Nijeriya, saboda al’adu.

Alake ya bayyana cewa majalisar zartarwar ta amince da wani sabon shiri na inganta tsari da kuma dakile asarar kudaden shiga a fannin ma’adinai.

A wani bangare na shirin, ya ce gwamnati za ta tura fasahar tauraron Dan’adam don sa ido kan muhimman wuraren hakar ma’adinai da kuma bin diddigin ayyukan ma’adani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: An mika fayil ɗin haɗin gwiwa tare da Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ga kwamitin koli na tsaron ƙasa

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a wata ganawa da jakadun kasashen waje da na kasa da kasa cewa: Iran bangare ce a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta “NPT” kuma tana yin aiki da tanade-tanaden da aka yi mata, amma idan aka yi la’akari da sabbin yanayi da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, hadin gwiwarta da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA za ta dauki wani sabon salo.

Yayin da yake ishara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana ci gaba da tsayawa tsayin daka kan yarjejeniyar tsaron da aka kulla tsakaninta da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya, Araqchi ya ce: Hadin gwiwar Iran da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya bai tsaya ba, amma idan aka yi la’akari da sabbin yanayi da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, wannan hadin gwiwa zai dauki wani sabon salo. Wannan gaba ɗaya al’ada ce kuma ana tsammanin hakan.

Shugaban jami’an diflomasiyyar na Iran ya ci gaba da cewa: Kamar yadda dokar majalisar shawarar Musulunci ta tanada, daga yanzu, kwamitin koli na tsaron kasar zai gudanar da dukkanin hadin gwiwar da Iran za ta yi da hukumar ne kawai, kuma wannan majalisar za ta yi nazari tare da yanke hukunci kan kowane lamari da hukumar ta bukaci ci gaba da sanya ido a Iran. Za a gudanar da waɗannan bita tare da cikakken la’akari da lura cikin aminci da tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce; An Mika Batun Hakin Gwiwa Tsakanin Iran Da Hukumar IAEA Ga Kwamitin Kolin Tsaron Kasa
  • Gwamnatin Mauritaniya Ta Karyata Rahoton Cewa Shugaban Kasarta Ya Gana Da Netanyahu
  • Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • Najeriya Ba Za Ta Karbi ‘Yan Ci Ranin Kasar Venezuela Da Amurka Za Ta Kora Ba
  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025
  • Jihohi 10 Sun Kinkimo Bashin Naira Biliyan 417 Duk Da Karin Samun Kudaden Shiga
  • Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki