Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
Published: 19th, March 2025 GMT
Iran ta bakin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, Esmaeil Baghaei, ta yi kakkausar suka ga sabbin hare-haren da Isra’ila ke kai wa zirin Gaza, yana mai bayyana su a matsayin “ci gaba da kisan kiyashi da share wata al’umma a yankin da aka yi wa kawanya.
Baghaei ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar, sa’o’i bayan harin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwar daruruwan Falasdinawa da suka hada da mata da kananan yara.
Ya ci gaba da cewa, Amurka ce ke da alhakin kashe-kashen da ake yi a Gaza, yana mai cewa, ana kai hare-haren na Isra’ila ne da tare da goyan bayan Washington.
Baghaei ya kuma yi kira ga kasashen duniya da su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu, tare da dakatar da laifukan yaki da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza, wadanda ake aiwatar da su tare da cikakken goyon bayan Amurka, Birtaniya da sauran kasashen yammacin duniya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya kuma ce rashin yin magana a fili kan keta dokokin kasa da kasa da Isra’ila ke yi, zai gurgunta tsarin shari’a na ka’idojin da aka kafa bisa kundin tsarin mulkin MDD, yana mai gargadi kan illar da irin wannan yanayi ke haifarwa ga zaman lafiya da tsaro a duniya.
Baghaei ya kuma bayyana irin nauyin da al’ummar musulmi ke da shi, inda ya bukaci kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ta dauki kwararan matakai na gaggauta gurfanar da shugabannin Isra’ila a kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC), da kuma dakatar da bayar da tallafin makamai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka a kan kasar tamkar shelanta yaki ne.
Araghchi ya bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ya aikewa babban sakatare na MDD da kuma shugaban kwamitin sulhu bayan da Isra’ila ta kai munanan hare-hare kan wuraren soji da cibiyoyin nukiliya da kuma wuraren zama wanda ya yi sanadiyar mutuwar wasu manyan kwamandojin dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC), masana kimiyyar nukiliya da fararen hula na iran.
“Wadannan ayyuka na zalunci ba wai kawai sun zama babban cin zarafi ne ga ‘yancin kan kasar Iran a matsayinta na mamba mai cin gashin kanta a Majalisar Dinkin Duniya ba, amma kamar yadda dokokin kasa da kasa da dokokin jin kai na duniya, ciki har da yarjejeniyar Geneva, suka tanada wannan na daga cikin ayyukan wuce gona da iri da laifukan yaki.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi kira ga kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ya sauke nauyin da ke wuyansa, ya yi kakkausar suka ga wannan ta’addanci tare da daukar matakin gaggawa kan Isra’ila.
Ya kara da cewa “Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta yi aiki da cikakkiyar azama wajen kare ‘yancinta, al’ummarta da kuma tsaron kasarta. Wannan wani hakki ne da ba za a iya tattaunawa da shi ba.”
Daga cikin hare-haren da ta kai, Isra’ila ta kai hari kan Cibiyar Nukiliya ta Natanz da ke tsakiyar kasar Iran, wadda ke aiki karkashin cikakken kulawar Hukumar Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA), in ji shi.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya yi gargadin cewa hare-haren ta’addanci na gwamnatin Tel Aviv na jefa rayuwar fararen hular Iran cikin hadari tare da haifar da barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.