Iran : hare-haren Isra’ila a Gaza ci gaba da kisan kare dangi ne
Published: 19th, March 2025 GMT
Iran ta bakin kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar, Esmaeil Baghaei, ta yi kakkausar suka ga sabbin hare-haren da Isra’ila ke kai wa zirin Gaza, yana mai bayyana su a matsayin “ci gaba da kisan kiyashi da share wata al’umma a yankin da aka yi wa kawanya.
Baghaei ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar, sa’o’i bayan harin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwar daruruwan Falasdinawa da suka hada da mata da kananan yara.
Ya ci gaba da cewa, Amurka ce ke da alhakin kashe-kashen da ake yi a Gaza, yana mai cewa, ana kai hare-haren na Isra’ila ne da tare da goyan bayan Washington.
Baghaei ya kuma yi kira ga kasashen duniya da su dauki nauyin da ya rataya a wuyansu, tare da dakatar da laifukan yaki da gwamnatin Isra’ila ke yi a Gaza, wadanda ake aiwatar da su tare da cikakken goyon bayan Amurka, Birtaniya da sauran kasashen yammacin duniya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ya kuma ce rashin yin magana a fili kan keta dokokin kasa da kasa da Isra’ila ke yi, zai gurgunta tsarin shari’a na ka’idojin da aka kafa bisa kundin tsarin mulkin MDD, yana mai gargadi kan illar da irin wannan yanayi ke haifarwa ga zaman lafiya da tsaro a duniya.
Baghaei ya kuma bayyana irin nauyin da al’ummar musulmi ke da shi, inda ya bukaci kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da ta dauki kwararan matakai na gaggauta gurfanar da shugabannin Isra’ila a kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC), da kuma dakatar da bayar da tallafin makamai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
A cewarsa, wajibi ne shirin ya mayar da hankali kan burin cimma zamanantarwa irin ta gurguzu da nufin gina babbar kasa da samun ci gaba wajen farfado da ita. Shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar, wanda shi ne daftarin dake zaman jigon jagorantar ci gaba na matsakaici da dogon zango a bangaren tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin, yana zayyana baki dayan burikan kasar da manyan ayyuka da manufofin da ake aiwatarwa a dukkan bangarori cikin shekaru 5. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp