Aminiya:
2025-06-15@05:54:51 GMT

Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba

Published: 17th, April 2025 GMT

A karo na biyu a cikin mako guda, matatar mai ta Dangote ta sanar da rage farashin man fetur.

Daga ranar 16 ga Afrilu, 2025, farashin man fetur zai tashi daga N865 zuwa N835.

Wannan dai shi ne karo na biyu da aka rage farashin a cikin mako guda yayin da matatar man Dangote a baya ta rage farashin daga N880 zuwa N865 kan kowacce lita.

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu

Sai dai kuma, har ya zuwa ranar Laraba, farashin bai canja ba a galibin gidajen mai da suka haɗa da cibiyoyin sayar da man fetur na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL).

Yayin da ’yan kasuwa ke maraba da matakin da Dangote ya ɗauka na ragin, duk da haka sun bayyana ra’ayoyinsu daban-daban kan abin da suka kira, “raguwa ba bisa ƙa’ida ba” wanda ke nuna asarar a harkar kasuwancin.

Babban jami’in hulɗa da jama’a na kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Yanzu za a riƙa samun man fetur na Dangote a farashi kamar haka a duk gidajen sayar da man da suke da haɗin gwiwa da mu….”

Ya ce, manyan abokan hulɗa da suka haɗa da: MRS, AP (Ardova), Heyden, Optima Energy, Hyde da Techno Oil, za su riƙa ba da man fetur a kan Naira 890 kowace lita, ƙasa da N920 a Legas.

A Kudu maso Yamma farashin zai kasance N900 kowace lita, an rage shi daga N930 yayin da a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya farashin zai zama N910 kowace lita, an rage shi daga N940.

A Kudu maso Gabas, Kudu maso Kudu, da Arewa maso Gabas, farashin zai kasance N920 kowace lita, ƙasa da N950.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: AP Ardova Farashin man fetur rage farashin kowace lita

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Da yake maida martani, Mokwa ya ce gwamanti ta fara biyan bashin tallafin rage radadin ga ma’aikata. Ya ce za a ci gaba da biyan kudin ne kashi-kashi har zuwa nan da watanni hudu masu zuwa.

“Mun fara biyan bashin nira 35,000 ga ma’aikata. Illar kawai wasu ma’aikatu da suka kasance masu cin kashin kansu da suke biyan tallafin kai tsaye, misali, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.

“Amincewa da tallafin naira 35,000 ga ma’aikata shi ne mafita ta wucin gadi da gwamnatin tarayya ta yi kafin amincewa da mafi karancin albashi na naira 70,000.

“Wannan ya faru a cikin watanni biyar, amma kungiyar kwadago ta ce ba a fara biya a kan lokaci ba, yanzu kenan akwai bashin watanni biyar.

“A cikin tallafin na watanni biyar, mun biya na wata guda. Yanzu haka tallafin watanni hudu ne suka rage, kuma za a biya su daki-daki,” ya shaida.

Kazalika, Mokwa ya fayyace zare da abawa da cewar gwamnatin tarayya ta fara biyan albashi mafi karanci ga dukkanin ma’aikatu, rassa da sashi-sashi na gwamnatin tarayya.

“Dangane da biyan albashi mafi karanci kuwa, an aiwatar da shi ga dukkanin ma’aikatu,” ya kara tabbatarwa.

Idan za a tuna dai a watan Yuli ne Shugaban kasa Tinubu ya sanya hannu kan dokar mafi karancin albashi.

Sai dai, duk da amincewa da mafi karancin albashi, har yanzu akwai korafe-korafe kan cikakken aiwatar da shi daga jihohi da kuma tarayya baki daya kusan shekara guda kenan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Aliko Dangote Ya Sauka Daga Shugabancin Kamfanin Sukarin Dangote
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • Rashin wutar lantarki ya durƙusar da kasuwanci a Arewa Maso Gabas