Aminiya:
2025-09-17@23:26:07 GMT

Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba

Published: 17th, April 2025 GMT

A karo na biyu a cikin mako guda, matatar mai ta Dangote ta sanar da rage farashin man fetur.

Daga ranar 16 ga Afrilu, 2025, farashin man fetur zai tashi daga N865 zuwa N835.

Wannan dai shi ne karo na biyu da aka rage farashin a cikin mako guda yayin da matatar man Dangote a baya ta rage farashin daga N880 zuwa N865 kan kowacce lita.

Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta Ka dawo Najeriya ka magance matsalar tsaro —Obi ga Tinubu

Sai dai kuma, har ya zuwa ranar Laraba, farashin bai canja ba a galibin gidajen mai da suka haɗa da cibiyoyin sayar da man fetur na Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL).

Yayin da ’yan kasuwa ke maraba da matakin da Dangote ya ɗauka na ragin, duk da haka sun bayyana ra’ayoyinsu daban-daban kan abin da suka kira, “raguwa ba bisa ƙa’ida ba” wanda ke nuna asarar a harkar kasuwancin.

Babban jami’in hulɗa da jama’a na kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce, “Yanzu za a riƙa samun man fetur na Dangote a farashi kamar haka a duk gidajen sayar da man da suke da haɗin gwiwa da mu….”

Ya ce, manyan abokan hulɗa da suka haɗa da: MRS, AP (Ardova), Heyden, Optima Energy, Hyde da Techno Oil, za su riƙa ba da man fetur a kan Naira 890 kowace lita, ƙasa da N920 a Legas.

A Kudu maso Yamma farashin zai kasance N900 kowace lita, an rage shi daga N930 yayin da a Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya farashin zai zama N910 kowace lita, an rage shi daga N940.

A Kudu maso Gabas, Kudu maso Kudu, da Arewa maso Gabas, farashin zai kasance N920 kowace lita, ƙasa da N950.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: AP Ardova Farashin man fetur rage farashin kowace lita

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa

A ƙoƙarinta na  ƙara wayar da kan jama’a game da harkokin lafiya a birane da karkara na Malam Madori, majalisar ƙaramar hukumar ta horar da mata da ‘yan mata 50 kan tsafta a lokutan al’ada domin kare kansu daga cututtukan mahaifa.

Jami’in shirin, Malam Ali Haruna, ya ce an zaɓi mahalarta horon ne daga kowace gunduma ta yankin

A cewarsa, manufar horon ita ce koyar da mahalarta yadda za su samar da kariya yayin al’ada da kansu domin rage kashe kuɗi da kuma kare kansu daga kamuwa da cututtukan mahaifa.

Shi ma shugaban sashen ruwa da tsafta, Malam Shehu Sani Gwadayi, ya bayyana cewa tsafta na da matuƙar muhimmanci ga rayuwar ɗan adam domin inganta rayuwa da ƙarfafa garkuwar jiki.

A nasa jawabin, mataimakin shugaban sashen ruwa da tsafta, Malam Muhammad Abdullahi, ya yi wa mahalarta horon bayani kan muhimmancin tsafta yayin al’ada domin gujewa kamuwa da cututtuka.

Shugaban ƙaramar hukumar Malam Madori, Alhaji Salisu Sani Garun Gabas, ya shawarci mahalarta da su mai da hankali ga sashen aikace-aikace na yadda ake sarrafa audugar mata a gida yayin horon.

 

Usman Muhammad Zaria

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kammala Ziyarar Yini 3 A Ma’aikatar Kananan Hukumomin Jihar
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta