Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Injiniya Abdullahi Garba Ramat a matsayin sabon Shugaba kuma Babban Jami’in Gudanarwa (CEO) na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC). Haka kuma, ya naɗa  Abubakar Yusuf a matsayin Kwamishinan Harkokin Abokan Hulɗa, da Dr. Fouad Olayinka Animashun a matsayin Kwamishinan Kudi da Harkokin Gudanarwa.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan Harkokin Watsa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, shugaban ƙasar ya bukaci waɗanda aka naɗa su yi amfani da ƙwarewarsu wajen tabbatar da burin gwamnatinsa a fannin wutar lantarki.

Onanuga ya bayyana cewa  waɗannan nade-naden suna jiran tantancewar Majalisar Dattawa. Sai dai, domin kauce wa gibin shugabanci a hukumar, Shugaba Tinubu ya umarci Injiniya Ramat da ya fara aiki a matsayin mukaddashin shugaba kafin tantancewarsa, bisa tanadin doka.

Injiniya Ramat, mai shekaru 39, kwararre ne a fannin injiniyan lantarki, yana  kuma  da ƙwarewa a harkokin gudanarwa, yana da digirin digirgir (PhD) a fannin Gudanarwa ta Dabaru (Strategic Management).

 

Daga Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi

Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bada motocin aiki ga shugabannin hukumomi, jami’an tsaro da wasu manyan jami’an gwamnati a jihar.

An gudanar da bikin mika motocin ne a Fadar Gwamnati da ke Minna.

Gwamna Bago ya bayyana cewa wannan mataki na bayar da motocin aiki na da nufin tallafa wa harkokin sufuri da kara inganta gudanar da ayyuka yadda ya kamata.

Ya yabawa kwazon wadanda suka amfana da motocin a aikin gwamnati tare da bukatar su yi amfani da su bisa gaskiya da amanar da aka dora musu domin cimma nasarorin da ake bukata.

Cikin wadanda suka ci gajiyar tallafin akwai Shugabannin Hukumar Kula da Ma’aikatan Kananan Hukumomi, Hukumar Majalisar Dokoki, Hukumar Ma’aikata da Hukumar Kula da Binciken Kudade.

Sauran sun hada da Darakta Janar na Gyaran Makarantu, Babban Mai Binciken Asusun Kananan Hukumomi da Ma’aikacin Kudi na Fadar Gwamnati.

Gwamnan ya kuma mika karin motocin Hilux guda 20 ga hukumomin tsaro daban-daban domin karfafa ayyukansu a fadin jihar.

Aliyu Lawal.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Neja Ta Raba Motoci Ga Ma’aikata Da Hukumomi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Taya Ali Larijani Murnar Nada Shi Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran
  • Tinubu ya taya ’yan matan Yobe da suka lashe gasa a Ingila murna
  • Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Jihar Kano Ya Sha Alwashin Kawar Da Badala A Harkokin Fina-finai
  • Iran: An nada Larijani a matsayin sakataren kwamitin koli na tsaron kasa
  • Iran Ta Kafa Kwamitin Tsaron Kasa Wanda Zai Kula Da Sabbin Matsalolin Tsaro
  • Sashen Lafiya Zai Fara Amfani Da Sabuwar Fasahar AI Don Inganta Lafiya
  • FG Za Ta Raba Naira miliyan 3.4m Ga Wadanda Suke Amfana Da Shirin ACReSAL
  • Gwamnatin Tarayya Ta Karrama ‘Yan Wasan Kwallon Kwando Na Mata