Tinubu Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Kula Da Wutar Lantarki Ta Kasa
Published: 7th, August 2025 GMT
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Injiniya Abdullahi Garba Ramat a matsayin sabon Shugaba kuma Babban Jami’in Gudanarwa (CEO) na Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta Najeriya (NERC). Haka kuma, ya naɗa Abubakar Yusuf a matsayin Kwamishinan Harkokin Abokan Hulɗa, da Dr. Fouad Olayinka Animashun a matsayin Kwamishinan Kudi da Harkokin Gudanarwa.
A cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara ta Musamman kan Harkokin Watsa Labarai da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, shugaban ƙasar ya bukaci waɗanda aka naɗa su yi amfani da ƙwarewarsu wajen tabbatar da burin gwamnatinsa a fannin wutar lantarki.
Onanuga ya bayyana cewa waɗannan nade-naden suna jiran tantancewar Majalisar Dattawa. Sai dai, domin kauce wa gibin shugabanci a hukumar, Shugaba Tinubu ya umarci Injiniya Ramat da ya fara aiki a matsayin mukaddashin shugaba kafin tantancewarsa, bisa tanadin doka.
Injiniya Ramat, mai shekaru 39, kwararre ne a fannin injiniyan lantarki, yana kuma da ƙwarewa a harkokin gudanarwa, yana da digirin digirgir (PhD) a fannin Gudanarwa ta Dabaru (Strategic Management).
Daga Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu ya gana da Sarkin Musulmi a Aso Rock
Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, ya gana da Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja a ranar Juma’a.
Sarkin Musulmi, wanda shi ne Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci ta Najeriya (NSCIA), ya gana da Shugaban Ƙasa ba tare da ’yan jarida ba.
Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu — Tinubu Kamfanin wutar lantarki na Abuja ya salami ma’aikata 800Ganawar na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Shugaba Tinubu ya gana da Archbishop Ignatius Kaigama na Katolikan Abuja, a wani yunƙuri na inganta dangantakar addinai da zaman lafiya a Najeriya.
Ko da yake ba a bayyana abin da suka tattauna ba, amma ganawar ba za ta rasa nasaba da ƙarfafa fahimtar juna tsakanin addinai da kuma bunƙasa haɗin kan ƙasa da ci gaba.
Hakan na zuwa ne bayan shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin soji kan Najeriya bisa zargin cin zarafin Kiristoci.
Bayan ganawar, Sarkin Musulmi, ya raka Shugaba Tinubu zuwa sallar Juma’a a Masallacin Fadar Shugaban Ƙasa.
A lokacin huɗubar sallar Juma’ar, limamin masallacin, Alhaji Abdulwaheed Abubakar, ya yi kira ga ’yan Najeriya da su tallafa wa ƙoƙarin gwamnati na ƙarfafa zaman lafiya da tsaro.
Ya tunatar da jama’a cewa zaman lafiya shi ne ginshiƙin ci gaban al’umma da ci gaban ƙasa baki ɗaya.