Jami’ar Bayero Ta Bayyana Alhininta Bisa Kisan Gillar Wani Dalibinta
Published: 7th, August 2025 GMT
Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta bayyana alhinita kan kisan gilla da aka yi wa Umar Abdullahi Hafizi, dalibi da ke matakin karatu na 3 a Sashen Ilimin Zamantakewa (Sociology), wanda wasu masu kwacen waya suka daba wa wuka har lahira a gidansa da ke unguwar Dorayi a ƙaramar hukumar Gwale.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Hulɗa da Jama’a na jami’ar, Malam Lamara Garba, ya fitar, wacce aka rabawa manema labarai.
A cewarsa, kodayake lamarin ya faru ne a wajen harabar jami’ar, shugabannin BUK sun jaddada cewa suna kokari wajen tabbatar da tsaron ɗalibansu.
Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana wannan lamari a matsayin babban rashi da ya girgiza al’ummar jami’ar, tare da mika ta’aziyyarsa ga iyalan mamacin, abokansa da ɗaliban jami’ar baki ɗaya.
Farfesa Abbas ya ce jami’ar na aiki kafada da kafada da hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan danyen aiki sun fuskanci hukunci.
Daga cikin matakan gaggawa da jami’ar ta ɗauka, sun haɗa da jigilar gawar mamacin zuwa garinsu na Zariya a Jihar Kaduna domin yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci.
BUK ta kuma shawarci ɗalibai da su zauna lafiya da yin taka-tsantsan, tare da kira ga jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro da bayanan da za su iya taimaka wa binciken da ake ci gaba da yi.
Jami’ar Bayero ta yi addu’ar Allah ya jikan Umar Abdullahi Hafizi, ya kuma bai wa iyalansa juriyar wannan babban rashi.
Daga Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp