Aminiya:
2025-11-08@18:35:55 GMT

An kama bama-baman da aka boye a cikin kayan gwangwan a Kaduna

Published: 7th, August 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna ta kama wasu bama-bamai da ba su fashe ba da wasu tarin makamai da aka shigar da su jihar cikin kayan gwangwan daga jihar Borno.

Lamarin dai ya jefa fargaba a zukatan mutane kan yadda kayayyaki ke yawo babu bincike daga jihohin da ke fama da rikici.

Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari Bai kamata ake bai wa ɓarayi muƙamin ministoci ba — Sarki Sanusi II

Kakakin rundunar a jihar, DSP Mansir Hassan ne ya tabbatar da hakan, inda ya ce an kama kayan ne ranar Asabar bayan wasu bayanan sirri da rundunar ta samu.

Ya ce an samu kayan ne a cikin wani kamfanin da ke hada-hadar kayan gwangwan da ke rukunin masana’antu na Kudandan da ke karamar hukumar Kaduna ta Kudu.

“Wasu kwararrun jami’anmu daga sashen da ke kula da abubuwa masu fashewa ne ya je wajen bayan bayanan. Bayan cikakken bincike, an tabbatar da cewa kayan bama-bamai ne da ba su kai ga fashewa ba,” in ji Mansir.

Kakakin ya ce nan take jami’an nasu suka kwashe bama-baman zuwa wajen da ya dace sannan suka lalata su ba tare da sun fashe ba.

Ya kuma ce yayin aikin, dakarun sun gano makamai, cikin har da wata karamar bindiga kirar gida wacce ke makare da albarusai, da ma wasu tarin makaman.

Kakakin ya ce nan take Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabiu Muhammad ya bayar da umarnin rufe kamfanin da aka sami kayan domin a samu damar fitar da dukkan makaman ba tare da an bar ragowa ba.

Kwamishinan ya kuma gargadi masu sana’ar ta gwangwan da su daina kawo irin kayayyakin daga yankunan da suke fama da rikici zuwa jihar ta Kaduna.

Ya kuma ce yanzu haka suna ci gaba da bincike domin gano tushen makaman da kuma dalilin shigo da su cikin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda

এছাড়াও পড়ুন:

 Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan

Tarayyar turai ta bayyana cewa ma’aikatan Agaji ba za su iya isha cikin garin Al-fahar ba,kuma birnin ya zama tamkar makabarta.

Tarayyar turai din ta  bakin mai Magana da yawunta Eva Herneserova ta kuma ce; Sudan ta zama daya daga cikin kasashen da gudanar da ayyukan agaji ya tsananta a duniya,kuma har yanzu da akwai fararen hula da aka killace su adaidai lokacin da ake ci gaba da kai wa asibitoci hare-hare.

Eva Herneserova ta kuma ce; Babu sauki ko kadan a kokarin shiga cikin birnin domin isar da kayan agaji.

Ma Magana da yawun kungiyar tarayyar turai din ta kuma yi gagradi akan cewa bai kamata a rika amfani da yunwa da kuma kisan kiyashi a matsayin makamin yaki ba,domin hakan yana a matsayin take dokokin kasa da kasa ne na ayyukan agaji.

Haka nan kuma ta yi kira ga dukkanin bangarorin da suke fada da juna da koma kan teburin tattaunawa da kuma tsagaita wutar yaki.

Rundunar kai daukin gaggawa ta  RSF kwace iko da birnin Al-fasha, bayan da killace shi na tsawon watanni 18. A yayin da mayana rundunar ta RSF su ka shiga cikin birnin sun aikata laifukan yaki da ya hada da yi wa fararen hula kisan kiyashi.

Bugu da kari, suna hana mutane ficewa daga cikin garin domin zuwa inda za su sami aminci.

Gwamnatin Sudan tana zargin kasar UAE da taimakawa mayakan na RSF da makamai da kuma kawo ‘yan ina da yaki daga kasashen Columbia, Sudan Ta Kudu da Afirka Ta Tsakiya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Turkiya Ta Fitar Da Sammacin Kama Natanyaho Da Wasu Jami’ian Isra’ila Kan Yakin Gaza
  • Lalacewar Tarbiyar Dalibai Mata A Makarantun Islamiyya Da Na Boko
  • Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
  • Matsalar Tsaro: Mun samu gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  • Matsalar Tsaro: Mun sami gagarumin ci gaba a shekaru biyu – Tinubu
  •  Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan
  • Zaben Kananan Hukumomi A Neja Ya Bar Baya Da Kura
  • Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai
  • Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da tantance sabon Ministan Tinubu