Yadda kwacen babur da waya ya maye gurbin garkuwa da mutane a Birnin Gwari
Published: 7th, August 2025 GMT
Bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin tubabbun ’yan bindiga da jama’ar gari a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna, mazauna yankin sun ce yanzu matsalar tsaron ta dauki sabon salo.
A watan Oktoban 2024 ne dai aka kulla yarjejeniyar sulhun tsakanin bangarorin biyu.
Yarjejeniyar na zuwa ne bayan shafe sama da shekara 10 ana fama da rikicin da ya mayar da babbar hanyar Kaduna zuwa Birnin Gwari daya daga cikin mafiya hatsari a Najeriya.
Daga shekara ta 2015, mazauna yankin sun sha fama da hare-hare da garkuwa da su, yayin da matafiya kuma ala tilas suka koma neman rakiyar sojoji kafin su iya wuce hanyar.
Yanzu dai yankin ya fara samun saukin matsalar, yayin da mazauna yankunan suka fara komawa gidajensu manoma kuma suka ci gaba da noma gonakinsu.
To sai dai da alama yanzu a maimakon garkuwa da mutanen, rahotanni na cewa a yanzu ’yan bindigar sun fara yawo a gonaki suna kwace babura, wayoyi, kudade da ma kayan aikin gona daga hannun manoman yankin.
Mazauna kauyen Kuyello da ma wasu kauyukan sun ce yanzu suna zaman dardar.
Wasu daga cikinsu sun kyale gonakin gaba daya, wasu kuma sun ce yanzu sukan bar wayoyinsu a gida saboda tsoron za a iya yi musu fashi.
“Yanzu ’yan bindiga sun daina garkuwa da mutane, amma sun koma yi mana kwace. Yanzu suna yawo a gari hankalinsu kwance ba sa tsoron kowa,“ in ji wani mazaunin garin na Kuyello.
Hakan dai ya sake jefa tsoro a kan ingancin zaman sulhun da aka ce an yi.
Mazauna yankin dai sun yi korafin cewa babu wani yunkuri da ake yi na dakile tubabbun ’yan bindigar daga kwacen da suke yi, lamarin da ya sa suka ce suna tsoron sake komawa gidan jiya.
Bayanai dai na cewa yanzu matafiya na bin hanyar ta Kaduna zuwa Birnin Gwari, wacce babbar mahada ce tsakanin kudanci da arewacin Najeriya, ba tare da wata barazana ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birnin Gwari
এছাড়াও পড়ুন:
Mutanen Kasar Lebanon Suna Tsoron HKI Zata Shiga Kasar Daga Kasar Siriya
Jami’an tsaro a kasar Lebanon sun bayyana damuwarsu da yiyuwar sojojin HKI su farwa kasar da yaki da nufin kwace kasar da kuma sunan yaki da kungiyar Hizbullah.
Jaridar da nation ta kasar amurka ta bayyana cewa, HKI ta jibje sojojin masu yawa da kuma tankunan yaki a kusa da Jabal sheikh da suka mamaye, don mai yuwa ta fadawa kasar Lebanon ta kuma mamaye gabaci da areawacin kasar kafi ta fuskan kungiyar Hiszullah wacce tafi bada karfinta a kudancin kasar.
Wasu majiyoyin tsaro guda 2 a kasar ta Lebanon wadanda basa son a bayyana sunayen na fadar cewa sojojin HKI a kan iyakar kasar Lebanon da Siriya sun bayyana cewa a hankali a hankali sojojin HKI suna matsowa kusa da kan iyakar kasar da kasar Siriya.
Tun bayan faduwar gwamnatin Bashhar al-Asad jiragen yakin HKI sun ci gaba da yin luguden wuta a yankunan Bika na gabacin kasar Lebanon, wanda ya nuna irin shirin da suke na sake mamayar kasar ta Lebanon.
Jiragen yakin HKI sun kai hare-hare a kan garin Baalabak da yankin bika da sunan wargaza sansanonin cilla makaman Hizbullah.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Amurka ta Fara Janye Wasu Sojojinta Daga Wurare 3 A Kasashen Iraki Da Siriya August 7, 2025 Kasar Masar Tana Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka August 7, 2025 Araqchi: Ba a kayyade wani lokacin shiga wata sabuwar tattaunawa da Amurka ba August 7, 2025 Ghana: Ministocin tsaro da muhalli sun rasa rayukansu a hatsarin jirgi mai saukar ungulu August 7, 2025 Jamus: Shahararrun mutane da ‘yan jarida sun bukaci a daina baiwa Israila makamai August 7, 2025 Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya August 7, 2025 Pezeshkian Ya Jaddada Wajabcin Haduwar Kasashen Musulmi Wajen Hana Laifukan Yaki A Gaza August 6, 2025 Araqchi Ya Taya Larijani Murnar Zama Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran August 6, 2025 Japan: An Fara Juyayin Cikar Shekaru 80 Da Harin Amurka Na Makamin Nukiliya A Hiroshima August 6, 2025 Sudan: Dakarun RSF Sun Kashe Fararen Hula 14 Tare Da Jikkata Wasu Na Daban August 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci