Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Published: 7th, August 2025 GMT
“Ko da yake lamarin ya faru ne a wajen harabar jami’a, Hukumar Gudanarwa ta jami’ar na cikin jimami matuƙa da wannan mummunan lamari, kuma tana miƙa ta’aziyyarta ga iyalan marigayin, abokansa da sauran ɗalibai,” in ji sanarwar.
Shugaban Jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana cewa jami’ar na aiki tare da hukumomin tsaro domin a kama waɗanda suka aikata wannan laifi.
An binne marigayin a garinsu da ke Zariya a Jihar Kaduna.
Jami’ar ta buƙaci ɗalibai su kwantar da hankalinsu tare da kasancewa masu lura da abin da ke faruwa a tare da su.
Haka kuma ta roƙi jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro da duk wani bayani da zai iya taimakawa wajen gudanar da bincike.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ɗalibi
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Alhazai Sun Karrama DG Labbo Bisa Nasarar Hajjin 2025
Jami’an Alhazai na shiyya-shiyya sun karrama Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa nasarorin da aka samu a aikin hajjin shekarar 2025.
Shugaban jami’an alhazai na shiyya-shiyya, Alhaji Sale Haruna Kafin Hausa ya tabbatar da hakan a wani kwarya-kwaryan biki da aka gudanar a shelkwatar hukumar dake Dutse Babban Birnin jihar.
Ya ce karrama Ahmed Labbo, na da nasaba da gudunmawar da ya bayar da kuma samun nasarar aikin hajjin bana a gida da kuma kasar Saudi Arabia.
Yace wadannan nasarorin sun sanya hukumar ta samu lambobin yabo da kyautuka da dama a kasa mai tsarki.
Alhaji Sale Haruna Kafin Hausa, yana mai cewar jami’an alhazai na shiyya-shiyya suna alfahari da Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa yadda yake kula da su da kuma tafiya da kowa wajen gudanar da aikin hajji.
Da yake maida jawabi, Darakta janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yaba ma jami’an bisa wannan karamci da kuma gode musu bisa kokarin su wajen kula da alhazai a aikin hajjin bana.
Shima a nasa tsokacin, Mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara akan aikin hajji, Alhaji Isa Idris Gwaram ya bayyana Alhaji Ahmed Umar Labbo a matsayin Shugaba abun koyi da hukumar alhazai ta jihar take alfahari da shi.
Wakilinmu, ya shaida mana cewar, a yayin bikin an kuma karrama Daraktan kudi da mulki na hukumar, Alhaji Jamilu Ilu Kazaure wanda ya yi ritaya daga aiki.
Usman Mohammed Zaria